Connect with us

LABARAI

Masu zanga-zanga a Kano sun nemi a biya musu bukatu uku

Published

on

Zulaiha danjuma

Yayin da zanga-zangar juyin juya hali ta shiga kwana na hudu  a Kano, masu zanga-zangar #EndSARS, #Endbadgovernance da dangogin su sun nemi da a biya musu bukatu uku kafin su janye.

Kano Focus ta ruwaito masu zanga-zangar sun nemi gwamnati da ta kawo karshen mulkin kama karya  da kawo sauye-saye a ayyukan jami’an tsaron kasar nan da kuma  kawo karshen matsalar tsaro a arewacin Najeriya.

Matasan sun faro zanga-zangar ta yau litinin ne da misalin karfe bakwai na safe, da ga kan titin Sarkin yaki da ke unguwar Sabon Gari zuwa Faransa road suka bi ta  No mansland, zuwa Zungeru suka tike a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

da yake zantawa da Kano Focus guda cikin mansu zanga-zangar Ahmad Aminu ya ce sun fito ne domin su nuna rashin jin dadin su da yadda al’amura ke tafiya a kasar nan.

Ya ce lokaci ya yi da gwamnati za ta yi abin da ya da ce wajen gyara fasalin jami’n tsaron kasar nan.

Ita kuwa Fatima Sani cewa ta yi ita fa ta fito ke nan sai kuma yadda Allah ya yi da ita ko kuma gwanmati ta gyara rayuwa jama’a.

“Zamu ci gaba da yin zanga-zangar nuna adawa da masu garkuwa da mutane, da masu kisan jama’a ba gaira ba dalili, da kuma uwa uba boko haram” a cewar ta.

Ita kuwa Jane Mbah ta ce zanga-zangar ta wuce batun a kawo karshen SARS, sai dai batu ne na kawo karshen gwmnatin kama karya a kasar nan.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Hausa

Kano Pillars ta doke Katsina United 1-0

Published

on

Kano Pillars FC

Jamilu Uba Adamu

Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars ta samu nasarar doke Katsina United daci daya da nema (1-0 ) a fafatawar da suka yi yau Alhamis a filin wasa na Moshood Kashamu Abiola dake Babban birnin tarayya Abuja.

KANO FOCUS ta ruwaito cewa dan wasan Kano Pillars Auwalu Ali Mallam ne ya zura Kwallon a ragar Katsina United a ragowar mintunan da aka ware don karasa wasan.

Auwalu Ali Mallam

Idan za a iya tunatawa an daga wasan ne bayan da hatsaniya da ta barke ana tsakiyar wasa tsakanin kungiyoyin biyu a filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata a kwanakin baya.

Sai dai, a yau aka kammala wasan a filin wasa na Moshood Kashamu Abiola dake Babban birnin tarayya Abuja.

Hakan ya ba wa Kungiyar Kano Pillars damar darewa matsayi na goma sha shida acikin jerin kungiyoyi ashirin dake fafatawa a gasar ajin Kwarraru na Kasa.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending