KANUN LABARAI
Dalilai biyar da ya sa mata suka fi son namiji mai gemu
Zulaiha Danjuma
Mata a Kano sun bayyana dalilai biyar da ya sanya suka fi son namiji mai gemu fiye da wanda bashi da shi.
A hirar da Kano Focus ta yi da wasu ‘yan mata sunce nuna mutuntaka, kyawun fuska ra’ayi, sunna da kuma damar yin wasa da gemun na da cikin dalilan da suka sanyasu zabar maza masu gemu.
Nuna mutuntaka
Wata budurwa a nan Kano Farida Abubakar da ke sana’ar sayar da abinci ta ce duk cikin maza ba wanda ke burgeta fiye da mai gemu.

A cewar ta namiji mai gemu komai kankatarsa yana nuna mutuntaka yana kuma kara gyara shi.
A don haka ta ce matukar ita za ta zabi mijinta to shakka babu mai gemu zata zaba.
Ita kuwa Khadija Adamu da ke Jami’ar Bayero ta ce namiji mai gemu ba wanda ya kaishi kamala da cika ido da kuma nuna mutuntaka.
A don haka ita dai zabin ta shi ne namiji mai gemu ko da kuwa mummuna ne.
Kwanciyar rai
Haka zalika matan sunce namiji mai gemu ko ba komai a kwai shiga rai.
Zainab Ka’oji daliba a kwalejin kimiyya da ke nan Kano ta ce ita dai namiji mai gemu ya fi kwanta mata a rai ba tare da l’akari da kalar sa ba.
Ta ce namiji mai gemu yana matukar burgeta musasamn mai mai saje musamman ma idan yana kula da shi.
Ita kuwa Nusaiba Magaji da ke Unguwar Tarauni a nan Kano ta ce baa bin da za a yi da namiji mara gemu ko saje.
Ta ce namiji mai gemu ya fi shiga rai ya kuma fi sanya mace farinciki da zarar ta kalleshi.
A cewar ta mazan da basu da gemu basu da ko dadin kallo.
Ta kara da cewa namijin da bashi da gemo komawa yake kamar mace baya bada sha’awa ko kadan.
Kyawun Fusaka
Haka zalika wasu ba’arin yan matan sunce abin da yasa suka fi zabar namiji mai gemu shi ne sun fi wadanda basu da shi kyau.
Fatima Ibrahim da ke unguwar farm Center a nan Kano ta ce maza masu gemu suna da tsananin kyau fiye da shagirai.
Ita kuwa Farida Abubakar da ke unguwar Hauwasa a nan Kano ta ce ana ganin namiji mai gemuma a zahirin sa kaga kyayyakwa.
A don haka ta ce ita dai ta zabi mai gemu domin ko da yana da muni to gemun na boye munin sa.
Zaka iya wasa dashi
Ba’arin wasu yan matan kuwa cewa suke sun zabi namiji mai gemu ko dan su yi wasa da gemun.
Khadija Adamu dake Unguwar Kabuga ta ce babban abin da ya sanya ta zabi namiji mai gemu shi ne ko dan ta yi wasa da gemu iya son ranta.
A cewar ta idan mace tana da miji mai gemu to ko ya bata mata rai da ta fara wasa da gemunsa sai zuciyar ta ta sakko.
Sunnah
Haka kuma wasu ‘yan matan sun ce sun zabi mai gemu ne domin shi gemu sunna ne.
A cewar Ramatu Shehu ta zabi namiji mai gemu ne saboda cewar mafiya yawan masu ajiye gemu suna dabbaka sunnan ne.
Ko me mazan ke cewa game da ra’ayi matan?
Wasu daga cikin samari a nan Kano da Kano Focus ta zanta da su sun bayyana yadda suka tsinci kan su a hannun yan matan.
Mustapha Fagam dalibi ne a jami’ar Bayero da ke nan Kano ya ce ya ga mata ba adadi da zuciyar su ke kaunar namji mai gemu.
Ya ce mata sun sha gaya masa ra’yin su na son namiji mai gemu ko da kuwa mummuna ne.
Ya ce mata da dama ne suka guje shi sabo da bashi da gemu.
Shi kuwa Mustapha Rabi’u da ke sana’ar sayar da katin waya a unguwar Tudun Yola ya ce ya rabu da mata kusan biyar sabo da shi shagiri ne.
Mata nason gemu
A cewar Bashir Tahir Sulaiman mata da yawa na manne musu saboda gemun da suke dashi.
A cewar sa yadda mata ke masa saboda gemunsa na sa shi ya dan ji girman kai.
Ya ce hakan ta sanya ya tanaji mai da sauran kayan gyara domin ya ci gaba da burge matan
Shima Abdussalam Danjuma da ke zaune a unguwar zoo road ya ce mata na rububin sa saboda kyawun gemunsa.
Ya ce mata basa dauke ido da ga gemusa musamman ma idan ya sanya dogayen kaya da kuma hula.
Ya ce hakan ta sanya shi ya ke sanya mai domin gyaran gemun nasa yadda matan za su so shi sosai.
Said dai duk da wannan batu akwai matan da su kuma gemun bai damesu ba.
Maza masu gemu kazamai ne
Wata budurwa mai suna Khadija Nuhu Umar da ke unguwar hotoro
ta ce ko kadan namiji mai gemu baya burgeta domin maza masu tara gemu kazamai ne.
Ta ce mafiya yawan mata masu gemu haka suke barin sa butsa-tsa ba kyan gani da hakan ke sanya ta shirin yin amai idan taga mai shi.
Wata malamar jinya Asibitin koyar na Aminu Kano Hafsa Inuwa ta ce maza masu gome basa burgenta ko kadan.
A cewar ta masu tara gemu kazamai ne basa iya tsafta ce gemun nasu.
Ko da ya ke ana samun wasu suna wankewa amma duk da haka baya burgeta.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
