Connect with us

KANUN LABARAI

Lafiya jari: Illoli 10 da kaciyar mata ke haifarwa

Published

on

 

Zulaiha Danjuma

Wani kwarraren likitan mata da ke asibitin koyar na jami’ar Jos Dakta Kenneth Egwuda ya bayyana matsaloli goma da kaciyar mata ke haifarwa musamman ga ‘yan mata.

Yayin tattaunawa ta musamman da jaridar Kano Focus likitan ya ce kaciyar mata na jawo matsalar da ba safai ake iya maganceta ba.

A cewar sa matsalolin sun hadar da shigar cuta, karewar jini, wahala yayin haihuwa, da rashin haihuwar ma baki daya, sai kuma yoyon fitsari da kuma rauni yayin kaciyar.

Sauran sun hadar da Kaduwa, da daukewar sha’awa da kuma daukewar dararjar mace sai kuma mutuwa.

Shigar cuta

Dakta Egwuda ya ce yin kaciyar mata na gayyato cutuka iri-iri da kayayyakin da akayi amfani da su wajen kaciyar ke haifarwa.

Ya ce wasu cutukan da ake dauka sakamakon yin afani da karafan kaciyar sun hadar da cutar kanjamau (HIV), da cutar hanta da kuma ciwon sanyi.

“Dukkanin wadannan cutukan ba wadanda za a dauke su da wasa ba ne.

“Ba ko shakka mata na iya kamuwa da wadannan cutukan sakamakon yi musu kaciya.

Haka kuma matakur aka kamu da cutukan ba a dauki mataki da wuri ba shakka babu za a rasa rai.

Rasa jini

Likitan ya ce yiwa mata kaciya na jawo rasa jini a jiki da hakan ke jefasu cikin hadduran kamuwa da cutuka daban-daban .

“Rasa jini sakamakon yiwa mata kaciya shi ne mafarin bude Kofar kowacce cuta a tare da su.

“Babu yadda za a yi ka cirewa mace wani abu a matucinta ka ce jini ba zai fita, kuma fitar da ya ke yi yana saba ka’idar yadda ya kamata da hakan ke zama babban hadari a gare su”.

Wahala yayin haihuwa

Likitan ya ce matan da ake yiwa kaciya na fadawa cikin matsala ya yin haihuwa da ka iya sanyasu rasa abinda ke cikin su.

“Suna cikin hadari mai tsanani ya yin haihuwa musamman ma lokacin da suka zo turo jaririn su waje.

Hakan kuwa na faruwa ne sakamakon yadda aka yayyanka hanyar da jarin zai fito ya yi rauni harma ya zama tabo.”

Rashin haihuwa  

Dakta Ggwudu ya kara da cewa kaciyar mata na iya jawo rashin haihuwa ga mata sakamakon matsalolin da ake samu yayin saduwa.

Ya ce matan da aka yiwa kwaciya na samun matsala sosai wajen samun ciki da haihuwarsa.

“A wasu lokutan daukar ciki kan zame musu matsala saboda raunukan da aka riga aka yi musu yayin kaciyar.”

Yoyon fitsari 

Haka zalika likitan ya ce yoyon fitsari wata babbar matsalace da matan da aka yiwa kaciya ke fuskanta.

“Idan tsautsayi ya sa aka yanko mace da nisa har aka taba mahadar fitar fitsari to hakan na haifar da yoyon fitsari marar tsayawa.”

“A wasu lokutan musamman ma wanzamai na yankewa har su ta ba blader da hakan ke  haddasa ,matsala domin idan an yanke ba zai sake tofowa ballantan ya koma ya rufe.

Rauni  

Dakta Ggwuda ya ce tabon raunin da ka yiwa mata yayin kaciyar na ci gaba da girma a  gaban mace lokaci bayan lokaci da hakan ke tsuke musu gaba.

“Tudun tabban da ke samu na toshe Kofar gabansu sosai da har ta kai mazajensu ba za su iya biyan bukatun su da su ba.

A cewarsa hakan kan jefa matan cikin matsanancin hali da wasu lokutan man har sai an yi musu tiyata.

dauke sha’awa 

Likitan matan ya ce yiwa mata kaciya na rage sha’awar su ainun da hakan ke sanyawa suji basa bukatar saduwa da mazajensu baki daya.

Haka kuma ya ce a duk lokacin da mazajensu za su sadu da su suna fuskantar zafi mai tsanani da ke jefa su cikin damuwa.

Wannan kuma na taimakawa wajen daina shawa’awa baki daya.

Kaduwa

Likitan ya ce a mafiya yawan lokaci matan da aka yi wa kaciya na kaduwa ainun da hakan ke sanya su cikin damuwa a kowanne lokaci.

“Matan da aka yiwa kaciya na fadawa cikin damuwa tsahon rayuwarsu sakamakon yadda aka basu wahala lokacin yi musu.

“Kaduwar da suke yi lokacin da suke ganin yadda ake zurmuka musu karfe mai kaifi a gabansu, kuma suji ana yanka wani abu jikinsu na haifar da kaduwa mai yawa da galibinsu ke sanya su jijjiga

Rasa darajar ‘ya mace

liktan matan ya ci gaba da cewa kaciyar mata na sanya mata suji cewa sun koma ba ya, ba kamar sauran ma ta ba.

Ya ce matukar sauran mata ‘yan uwanta da suka san anyi mata kaciya to suna daukarta wata daban a cikinsu da hakan ke sayanta taji ta zama koma baya.

“Wannan na da alaka da yadda mace ke kallon kanta a matsayin wata marar daraja a cikin mata ko da kuwa tana da dararjar.

Mutuwa

Dakta Ggwuda ya ce mafi tsanani ga dukkan haduran da aka lissafa shi ne mutuwa.

Ya ce abu ne mai sauki mace ta rasa ranta sakamakon kamuwa da cutukan da ke tattare da yin kaciyar.

Mai ya kamata jama’a su sani

Dakta Ggwuda ya ce duk da cewa a yanzu matsalar ta ragu a birnin sai dai kauyuka, akwai bukatar a ci gaba da wayar da kan jama’a har a kawo karshen matsalar.

A cewarsa ko kadan kaciyar mata bata haifar musu da da mai ido ta kowacce fuska.

Haza zalika ya ce yiwa mata kaciya bashi da wata fa’ida ta bangaren lafiya face jefa lafiyar tasu cikin matsala.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending