Connect with us

KANUN LABARAI

IAR ta samar da irin masara da ke jure fari, kuma tsutsa ba ta ci

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Cibiyar nazari da bunkasa al’amuran noma ta jami’ar Ahmadu Bello wato Institute for Agricultural Research (IAR) ta ce nan da shekarar 2022 za ta fito da sabon irin masara da ke jure karancin ruwa kuma tsuta ba ta iya ci da ake kira TELA maize.

Kano Focus ta ruwaito shugaban cibiyar Farfesa Isyaku Muhammad ne ya bayyana haka ya yin taron jin ra’ayoyin manoma kan yadda za a rungumi sabuwar fasahar da ya gudana ranar Talata a Kano.

Farfesa Isyaku ya ce matukar manoma suka rungumi wannan sabuwar fasaha to shakka babu za su samu amfanin masara da ya zarta wanda suka saba samu idan sun yi noma.

Ya ce cibiyar ta dade tana nazari kan yadda za a samar da wannan iri da zai taka rawa wajen inganta noman masara, ya kuma taimakawa manoma rage kudaden da suke kashewa wajen nomanta.

Sabuwar fasahar mafita ce ga manoma.

Farfesa Isyaku ya ce sau dayawa akan zo da sabuwar fasaha, kuma yana da wahala al’umma su karbeta nan ta ke ba tare da jin dar ba.

Manoma ma ba a barsu a bayaba wajen kaucewa a abinda ba su sanshi ba.

A don hakanne ya bukaci manoman da kada zuciyarsu ta kadu, da zarar wannan iri ya fito, to su karba su gwada za kuma su ga nasarar da hakan zai haifar musu.

Ya ce idan manomi yana samu buhu ashiri a gonarsa da tsohon irin masara, idan aka samar da wannan na zamanin to manomi zai iya samu buhu 35 zuwa 40.

Sabuwar fasahar za ta magance yunwa a kasar nan

Haka zalika Farfesan ya ce idan manoma suka fara amfani da wannan iri, to ba shakka zai taimaka wajen samar da abinci mai yawa da zai yi maganin yunwa a kasar nan.

Ya ce hatta hanyoyin samar da kudin shiga a kasar nan za su habaka ta dalilin wannan sabuwar fasaha.

A cewarsa ana gudanar da sana’o’I da dama da suka hadar da abincin kaji da sauran abubuwa da masara.

Inda ya ce matukar za a bunkasa wadannan sana’o’I jama’ da dama za su samu aikinyi za kuma a fita daga kangin yunwa.

Ko me manona ke cewa?

Ko da ya ke wasu daga cikin manona da aka zanta da su ya yin taron jin ra’ayin sun nuna jin dadin su dangane da sabuwar fasahar amma suna bukatar akara fahitar da su muhimmancin wanna iri.

A cewar Yusuf Ibrahim zai yi amfani da wannan fasaha da zarar an fito da ita domin ya tantance tsaba da tsakuwa.

Ya ce ko shakka babu ya yarda da binciken kimiyya, kuma zai karfafi abin da zarar an fito da shi.

Shima Kabiru Isa manomine da ya halarci taron ya ce su dai sai sun gwada sun gani a zahir kafin su fara ammfani da sabuwar fasahar.

Ya ce zai ware gona guda a cikin gonakin sa idan sabon irin ya fito ya kuma gwada, idan ya bashi yadda ake fada to ko shakka babu zai rungumi fasahar ka’in da na’in.

Ko menen amfanin TELA maize

La’akari da cewa adadin al’ummar kasar nan ya kai miliyan 200, Najeriya na bukatar a kalla tan miliyan 20 na masara domin ciyar da al’ummar kasarta.

Ko da ya ke rahotanni sun bayyana cewa Najeriya ce kasar da ta fi kowacce noman masara a nahiyar Afrika.

Amma ko a shekarar 2019 Najeriya ta samar da tan miliyan 18 ne kawai, da hakan ke nuna har yanzu dai ba a iya noma masarar da za ta wadaci ‘yan kasa.

Hakan ta sanya dole kasar nan ke laruwa da shigo da masara da ga kasashen ketare domin cike gibin da ake shi.

Haka zalika masana na gani sai an shigo da kimiyya wajen magance matsalar karancin masarar da ake da shi a kasar nan.

Hakan ce ta sanya cibiyar (IAR) ta tsunduna bincike a bangaren kimiyyar sauya sarrafa halitta wato (Biotechnology)

Cibiyar ta yi nazari kwarai kan yadda za a samar da sabon irin da zai taimaka wajen magance matsalar karancin masarar.

A karshe dai ta fito da wannan sabuwar fasaha ta Tela maize, wani sabon irin masara da aka kirkira da zai jure karancin ruwa, ya kuma ya ki tsutsa, ya kuma samar da amfani mai yawa fiye da wanda aka saba gani.

Haka zalika cibiyar IAR a yanzu ta dukufa wajen ganin an samarwa da manoma wannan iri da zai taimaka wajen kawo karshen karancin masara a kasar nan.

Amfanin sa

Sabon irin zai taimaka wajen rage kudaden da manoma ke kashewa wajen noma masara.

Haka irin yana yabanya me kyau ko babu wadataccen ruwa a inda aka shuka.

Haka zalika irin yana yaki da duk wata tsutsa da ke cin masara, ma’ana ita wannan masarar tsutsa bata kamata.

Sanna sabon irin yana kara adadin kwayar masarar fiye da wace ake samu idan an yi shuka ba da irin ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending