Connect with us

KANUN LABARAI

Muhimman abubuwan da suka faru a Kano cikin shekarar da muke bankwana da ita

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

A yayin da muke bankwana da shekarar 2020 Kano Focus ta yi nazari kan muhimman abubuwan da suka faru a jihar Kano da al’umma ba za su mace da shi ba.

Shekarar 2020 shekara ce da ta zo da sammatsi iri-iri da suka dagula lissafin al’umma da tabbas jama’a za su dade suna tuna ta.

Zuwan baturiya Kano

Janine Sanchez Weds Sulaiman Isa Isa

A cikin watan Janairun shekarar da muke bankwana da ita ne wata baturiya mai suna Janine Sanchez ta zo Kano domin auren wani matasi dan asalin unguwar Panshekara da ke nan Kano.

Zuwan baturiyar dai ya jawo ce-ce kuce a tsakanin al’umma, inda wasu ke ganin sa ce ta zo yi, yayinda wasu ke ganin wata bukata ce da ita akan sa ya sanya ta biyo shi.

Haka zalika wasu ba’arin al’umma na ganin cewa kwadayi ne irin na Sulaiman ya sanya shi soyayya da baturi.

To koma dai mene yanzu haka an dauran auren Sulaiman da baturiya kuma sun koma kasar Amurka.

Bude kotun daukaka kara a Kano

A rananr 11 ga watan Fabrairun shekarar da muke bankwana da ita ne aka bude kotun daukaka kara a Kano.

Shugabar kotun daukaka kara ta kasa Zainab Bulkacuwa ce ta jagoranci bude kotun domin saukaka al’amuran shari’a a kasa.

Haka zalika bayan da aka bude kotun an turo mai shari’a Abubakar Datti Yahya a matsayin alkalin kotun, yayin da mai shari’a Habib Adewale da kuma A.A Wambai za su dafa masa.

Idan za a iya tunawa kafin bude kotun, sai anje Kaduna ko wata jihar kafin a daukaka kara akan dukkan wata shari’a, amma da aka bude kotun an samu sauki kan wannan.

Tube Sarki Sunusi

A ranar 9 ga watan Maris din shekarar da muka yi bankwana da ita ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya tunbuke Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II.

Gwamnan ya ce ya dauki matakin tunbuke Sarkinne bayan da ya samu amincewar dukkanin ‘yan majalisar Zartaswarsa.

Haka zalika ya ce ya tunbuke sarkinne domin a kare mutunci da al’ada da kuma addini da ya yi zargin sarkin na watangaririya dasu.

Aminu Ado ya zama sarki

A dai wannan rana da aka cire Sunusi ne kuma aka sanar da Aminu Ado Bayero a matsayin sabon Sarkin Kano.

Anjiyo sakataren gwamnatin jiha Alhaji Usman Alhaji na cewa an zabi Aminu Ado a matsayin sabon Sarkinne domin cancantarsa da kwarewarsa akan sha’anin mulki.

Kafin nada shi Sarkin Kano shi ne Sarkin Bichi na farko a tarihi tun da aka kafa masarautar.

Idan za a iya tunawa Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya kirkiri sabbin masarauti hudu baya ga ta Kano inda ko wacce ya yi mata sabon sarki.

Bullar Korona a Kano

A rananr 11 ga watan Afrilun shekarar 2020 ne aka fara samun bullar cutar kwarona a Kano.

Rahotanni sun ce wanda aka fara samu din ya shigo jihar  Kano ne daga Birnin tarayya Abuja.

Haka kuma bayan an gwadashi ne aka killace shi a inda aka tanada domin killace masu dauke da ita a asibitin Kwanar Dawaki.

Kuma tun da ga wannan lokacine aka ci gaba da samun bullar cutar har zuwa wannan lokaci.

Buhari ya kulle Kano

A ranar 27 ga watan Afrilun shekarar da muka yi bankwana da ita ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya dokar kulle a jihar Kano ta sati biyu saboda bullar cutar Covid-a19 a Kasa.

Shugaban kasar ya ayyana dokarne lokacin da yake bayani ga al’ummar kasa kan halin da ake ciki dangane da cutar Covid-19.

Ya kuma bukaci al’umma da su zauna a gida ba shiga ba fita ba mu’amala da juna tsahon wadannan kwanaki.

Mace-macen Kano

A watan Afrilun shekarar bara ne dai aka dinga samu yawaitar mace-mace a Kano da aka kasa gane dalilinsu.

Sai dai wani likita a nan Kano Isa Abubakar ya ce mace-mace na afkuwa ne saboda dalilai guda uku.

Na daya zai iya kasancewa masu dauke da cutar Korona ne da ba a gwada an tabbatar da su ba.

Na biyu akwai mutane masu bukatar kulawar gaggawa ta likita amma saboda bullar Korona anyi watsi dasu.

Sai na uku ya ce marasa lafiya da yawa na kasa zuwa asibiti saboda kulle, suma kuma asibitocin basa karbarsu.

Soke bukukuwan salla

A ranar 18 ga Mayun shekarar bara ne gwamnatin Kano ta ce ta suke dukkanin shagulgulan Sallah sakamako bullar annobar Korona.

Ko da ya ke gwamnati ta bada kofa aje masallacin idi a yi salla amma da sharadai masu tarin yawa.

Karo biyu ke nan a wanna shekara ana hana bukukuwan salla, da ya hadar da  na sallah karama da kuma babbar sallah

Mutuwar Umar Sa’idu Tudun Wada

A ranar 30 ga wantan Yuni ne fitaccen dan jaridar nan na Kano Umar Sa’idu Tudun Wada ya rasu sakamakon hadarin mota.

A cewar makusacin sa Umar Sa’idu Tudun Wada ya yi hasashen mutuwasa  mako guda kafin ya rasu.

A cewarsa hakan ce ta sanya yayi ta aikata abubuwan alheri daf da rasuwar tasa domin neman kusanci ga Allah ta’ala.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending