Connect with us

KANUN LABARAI

Lafiya jari:Ko mene ne alaƙar cin goro da hawan jini

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Goro ɗan itaciya ne da ake amfani da shi domin ci, haka nan alama ce ta karrama baƙo yayin bukukuwa da sauran taruka, musamman a al’adun Najeriya da sauran ƙasashen Afrika ta yamma.

Bugu da ƙari ana amfani da shi a abubuwan sha domin ƙarin ɗanɗano.

Goro na ɗauke da sinadarai da dama da ake alaƙanta su da amfani kamar haka

Wartsakarwa: masu cin goro na amfani da shi domin wartsakewa, ƙara kuzari ko karsashi.

Maganin bacci ko kasala: saboda sinadarin kafin (caffeine) goro na iya rage jin bacci ko kasala.

Maganin tashin zuciya: ana amfani da goro domin magance matsalar tashin zuciya, musamman mata.

Dankwafe sha’awar abinci: Cin goro yayin jin yunwa na da tasirin rage sha’awar cin abincin ko jin matsananciyar yunwa.

Sauran amfanin goro da ke da alaƙa da lafiya

Rage raɗaɗin ciwon ɓarin kai (migraine).

Kashe ƙwayayyakin cuta a jiki.

Taimakawa masu ciwon asma(asthma) wajen buɗe hanyoyin numfashi.

Sai dai duk da waɗannan alfanu da bincike ke alaƙanta goro da shi, bincike ya nuna cewa; baya ga sauran sinadaran da ke cikin goro, goro na ɗauke da sinadarin kafin(caffeine) kaso 2 – 3 cikin ɗari.

Kuma bincike ya yi nuni da hauhawar jini bayan cin sinadarin kafin da ke cikin goro.

Sai dai hauhawar jinin ya fi ƙarfi ga masu cin goron a karon farko ko kuma masu ci jifa-jifa.

Haka nan hauhawar jinin zuwa na wani ɗan lokaci ne da sinadarin kafin zai ƙare a jiki.

Amma waɗanda suka shafe shekara da shekaru suna cin goron, jiki kan jure tasirin sinadarin kafin yau da gobe.

Saboda haka tasirin sinadarin kafin a kan hauhawar jini na raguwa ne da tsawon lokacin da aka daɗe ana amfani da shi.

Sai dai kuma wani bincike ya sake yin nuni da cewa ga masu hawan jini; amfani da goro yayin da ake shan magungunan hawan jini na da tasirin rage aikin maganin, musamman jinsin maganin hawan jini da ke rufe hanyar kalsiyam(Calcium channel blockers) wanda ke taimakawa wajen buɗa hanyoyin jini.

Bayan goro, sinadarin kafin na nan a cikin kofi(coffee), lemukan roba/gwangwani da baƙin shayi, har da ma wasu magungunan ciwo kai, mura, da kasala da ake saye a kasuwa.

Mafi kyawun al’amari tsakatsakinsa, saboda haka zai fi kyau a yi amfani da goro yayin buƙata kaɗai, amma ba ya zama ɗabi’ar kullum ba.

Sannan ga masu hawan jini, saboda hauhawar jini da sinadarin kafin ke kawowa, da kuma dankwafe tasirin jinsin wancan maganin hawan jini, zai fi kyau su ƙaurace wa cin goro, da sauran abubuwan da ke ɗauke da sindarin kafin.

Wannan bayani ba zai zamo a madadin tuntuɓar likitan ka/ki ba dangane da cin goro ko kafin.

 

Wannan bayani Kano Focus ta kwafo ne daga shafin Physiotherapy Hausa, mallakar asibitin koyarwa na Abdullahi Wase da ke nan Kano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Trending