Hausa
Ba za mu janye daga tuhumar Aduljabbar ba- Malaman Kano

Mukhtar Yahya Usman
Gamayyar Malam Kano da suka hadar da ‘yan Izala da na Tijjaniyya da kuma Kadiriyya sun ce suna nan kan bakansu, ba za su janye daga tuhumar Abduljabbar Kabara ba.
Kano Focus ta ruwaito gamayyar malaman sun cimma wannan matsaya ne ya yin zaman gaggawa da suka gudanar a masallacin Usman bn Affan da ke kofar Gadon Kaya da yammacin ranar Asabar.
Malaman da suka gudanar da zaman sun fito ne daga dukkanin bangarorin akida da ke jihar nan, da suka hadar da Izala da Qadiriyya da kuma Tijjaniyya.
Da yake jawabi a madadin malaman Dakta Muslim Ibrahim wanda shi ne shugaban zaman ya ce ko kadan ba za su janye shirinsu na tuhumar Abduljabbar ba.

Ya ce tunda kotu ta dakatar da zaman, kuma gwamnatin Kano ta karba, to za su jira lokacin da kotun za ta bada dama a gudanar da mukabalar.
A cewarsa basu ji dadin matakin da kotun ta daukaba, amma za su yi biyayya ga umarnin kotun har zuwa ranar 22 ga Maris da kotun ta sanya domin ci gaba da sauraron karar.
Ba zan taimakawa Abduljabbar ya yi suna ba -Sarkin Musulmi
Tuhumar Abduljabbar za a yi ba mukabala ba-Sheikh Ibrahim Khali
Masoyana ku janye karar da kuka kai Ganduje-Abduljabbar Kabara
Dakta Muslim ya kuma yi kira ga gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da kada ya janye kudirinsa na mukabalar, a cewarsa ta haka ne za a tsamo jama’a daga halaka.
“Muna cikin shirin ko ta kwana na zaman tuhuma.
“Muna jiran kotu ta baiwa gwamnati damar ci gaba da wannan shiri nata
“Muna tabbatarwa da kowa babu komai cikin wannan tuhuma fa ce alkhairi, don warware duk wata shubuha, ya taimakawa mutane fitda daga duhun bata da zandiganci.
“Muna tabbatarwa da gwamnati da duk wani mai fatan alheri ga al’umma cewa mu masu biyayya ne ga duk wani tsari da zai wanzar da zaman lafiya da ci gaban al’ummar Manzon Allah
Ba musan manufar lauyaba
Haka zalika malaman sun nuna bacin ransu ga lauyan da ya shigar da karar ya nemi a dakatar da zaman.
A cewar Dakata Muslim basu san manufar lauyan na shigar da karar ba kuma basu san wa ya dauki nauyinsa ba.
a cewarsu sai da ya dubi ranar juma’a daf da za a yi zaman sannan ya yi karar da ta ruguza komai.
A don hakan ne suka kirashi da ya ji tsoron Allah ya sani zai tsaya gaban Allah ya kuma amsa tambayar abinda ya aikta.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Hausa
Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Mukhtar Yahya Usman
The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.
Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.
He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.
“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.
