Connect with us

Hausa

Dalilai 4 da ya hana Teloli samun dinki a bana

Published

on

Zulaiha Danjma

Teloli a jihar Kano sun koka kan karancin dinkin sallah da jama’a ke kawo musu, biyo bayan matsin rayuwa da ake ciki.

Kano Focus ta rawaito cewa Telolin sun bayanna dalilai hudu da ke kara ta’azzara rashin samun aikin.

Cikin kuwa har da karin kudin kayan dinki, Rashin kudi a hannun jama’a, dawurwuran tsayar da zabi, da kuma rashin samun albashi.

Karin kudin kayan dinki

A cewar wani tela Abdussalam Kabir da ke dinki a unugwar Rijiyar Zaki, kudaden da tela yake siyan kayan dinki sun yi tashin gwauron zabo.

“A gaskiya komai ya canza, saboda tsadar kayan dinkin, samun dinki ya ragu”

“Wasu abubuwan da ake siya  ada N600 yanzu ya koma N800

“Me dinka set 4 ada da wuya yanzu ya dinka kala daya” Acewarsa.

Shi ma wani tela Kabiru Abubakar da ke Tudun Maliki  ya ce kudaden siyan kayan aiki a bana sun nunka.

“Kudin siyan kayayyakin dinki sun karu gaskiya, wasu sun ninka kudinsu akan yadda aka sansu”

“Kananan kamar zare wani dan N40 ya dawo N50, kuma quality na kayan ma duk  sun ragu.

“Shi komai da komai yadda aka sanshi ya ragu a quality ga kuma kudin sa ya karu” Acewar sa.

Rashin kudi 

Telolin sun cigaba da cewa rashin kudi na hana abokan huldarsu  kawo dinki.

Kabiru Muhammad ya ce, masu kawo dinki sun sauya daga yadda suka saba kawowa ba kamar a baya ba.

“Idan kostoma ada na kawo kaya kala 3, yanzunma zai iya kawo ukun amma za kaga darajar kanyan sun ragu.

“Alalmisali ace  bara sun kawo maka shadda me tsada wanda duk yadi zai iya kaiwa 2,500 zuwa 3,000 yanzu sai an rage kudin.

“sai ka gama mutum yaje ya siyo yadi, irin su Lana ko Kashmir ko irin su dan Aba dan ya samu rarar kudi.

“Wannan ragowar canjin da aka samu zai iya biyan kudin dikin dasu”

Haka zalika, Abdulsalam Muhammad ya ce “yara ma da iyayensu ke dinka musu kala 4 ko 3 yanzu da wuya a yi musu kala 2 saboda ba kudin”

“Kusan dai duk wanda ya kawo dinkin yaransa ba sama da guda biyu-biyu” Acewar sa

Rashin takamai-mai

Haka zalika Telolin sun bayyana cewa mafi akasari magidanta na shiga halin dawurwura da rashin takamai-mai wajen zabin mai za su dinka da iyalansu.

Wasu na tuna ni biyu, tsakanin dinkin da wasu al’amuran na gida wanne ne ya fi amfami.

“Mafi akasari ta abinci ake bata sutura ba, wani gani yake mai zai yi, shin dinkin ya kamata ya yi, ko abincin yara yakamata ya siya, ko kudin makarantar yara zai biya.

“Irin wannan matsololin da suke faruwa shi ne yake sa muke fuskanta karancin kawo dinki”

“Amma duk da hakan mutane na yin iya bakin kokarinsu wajen ganin sun yi ma kansu da iyalen su sutura” Acewarsa, a cewar Kabiru tela.

Rashin Albashi 

Telolin sun bayyana cewa  rashin biyan albashi na sanya jama’a kasa kai musu dinky, tunda galibin al’umma yan albashi ne.

“Gaskiya wannan lokacin ana samun karancin samun kayan dinki musamman ma wasu ba a biya albashi ba.

“Wani yana jiran sai an biya, inda zai iya kasancewa sai karshe-karshen azumi za a biya, kuma lokacin wani ma zai tunanin dinkin”

Shi ma Kabiru tela yace “Wasu rashin albashi ne da wuri, wani za kaga gwamnatin ta ba da albashin amma ta cire wani baa’ari daga ciki.

“Wani lokacin ma ba a biya albashin akan lokaci ba ko dai wasu abubuwa makaman cin haka” Acwarsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Trending