Hausa
Zawarawa ne ke sanya Abaya-Masana
Aminu Abdullahi
Batun Abaya ya mamaye kafafen sada zumunta musamman twitter tun bayan shigowar watan Ramadan ta yadda ‘yan mata ke nuna sha’awarsu ta ganin sun sanyata yayin bikin karamar Sallah.
Batun ya janyo barkewar muhawara tsakanin ‘yan mata da samari, inda wasu matan ke da ra’ayin yin Abaya koma ta wane hali ya yin da wasu kuma suka bayyana rashin gamsuwarsu na yin Abayar saboda wasu dalilai da suka bayyana.
Sai dai wani masanin zamantakewar Dan Adam da ke jami’ar Bayero a nan Kano Aminu Sabo Dambazau ya ce sanya Abaya alamu ne da ke nuna cewa mace Bazawara ce.
Ya ce a zamanin baya mata na sanya ta ne domin su rufe jikinsu sabanin yanzu da ta canza manufa.
Ya ce anyiwa Abayar fassara, cewar idan mace ta sakata hakan na nufin ta taba yin aure ta fito ne, kuma tana neman wani mijin.
“Idan kaga mace tasa Abaya ta fito titi to bazawara ce da take neman mijin aure, wata kuma ta saka ne kawai don ta ja magana,” a cewar sa.
Ya ce dabi’a ce ta dan Adam san birgewa musamman mata wanda hakan ne yasa suke gasa don ganin sun kere sa’a ba tare da sanin
To sai sai Kano Focus ta yi nazari kan yadda batun Abaya a kafafen sada zumunta ya dauki sabon salo na izgili da zargi a tsakanin matasa.
Me ya ja hankalin mata son kwaliyyar Abaya da sallah.
Abaya ba bakuwar sutura ba ce, mata sun jima suna sanyata tun lokacin da ba ta zama gama gari ba, kuma ainihi shigar ta samo asali ne daga larabawa.
Sai dai batun a bayar ya zama abin da a kafi tattaunashi a shafin twitter da ya bazu zuwa sauran shafukan sada zumunta.
Hakan yasa da yawan ‘yan mata ke da burin ganin sun mallaketa don ganin cewa suma ba a barsu a baya ba.
Wannan dai ya sanya samari tofa albarkacin bakinsu a kan lamarin wanda hakan yasa batun Abayar ke neman canza salo.
Wasu samarin sun wallafa rubuce rubuce daban daban da ke tattare da zargi da kuma rashin tabbas ga wadanda ke da burin sanya Abaya da sallah.
Ya yinda wasu samarin ke ganin batun Abayar ka iya zama wata hanya ta rabasu da masoyan su ko kuma haddasa fitina tsakanin mijin da bashi da halin yin Abayar da matar sa.
Ya yin da wasu kuma ke ganin cewa akwai matan da za su iya bin hanyar banza don cika burin su na samunta.
Ra’ayoyin mata
Kano Focus ta jiyi ra’ayoyin wasu mata kan batun yin a baya da karamar sallah.
Sadiya Ibrahim Mai shekaru 25 a unguwar Kofar Famfo cewa tayi za tayi yayin Abaya kamar yadda taga da yawan mata ita za su yi.
Ta ce a cikin kayan da za ta saka da sallah saida ta fadawa mahaifin ta ya hado mata da a baya.
“Ni dama ina sakawa to kuma naga yanzu wannan sallar ita za ayi ya yi shiyasa nima na fadawa mahaifina ya siyamin,” a cewar ta.
Ummukulsum Abubakar mai shekaru 20 ta ce tanaso tayi Abaya da sallah amma ba ta da hali.
“Inaso na saka amma irin wacce ake cewa za a yi yayin ta gaskiya tayi tsada sosai don suna maganar kudin ta ya kai dubu 20.
“Ni kuma ba za a iya siyamin riga kawai ta dubu ashirin ba amma idan saurayi na ya bani zan karba tun da shi yayi niya,” Inji ta.
Ta kara da cewa tana rage kudin makarantar ta koda an siya mata mara tsadar to za ta yi ciko don a canza mata.
Kadija Ahmad Sanusi da ke unguwar koki mai shekaru 26 cewa tayi “Maganar gaskiya bani da ra’ayin Abaya, tana burgeni amma ni indai abu ya zama gama gari to bazan yi shiba.
“Sabida mafi yawanci Abayoyin yanzu robane asaka dan gyalen ta ayi rolling a fita haka kuma nasan akwai illar da take tattare da ita shiyasa shaidan yake kawata wa mutane ita a idanuwan su,” a cewar Kadija.
Ta kara da cewa wasu ba siya suke yiba, basu akeyi wasu kuma koda basu da hali suna sanyawa kansu ne cewa dole sai sunyi.
Sadiya Bello Abdullahi da ke Hotoro ta ce tun kafin a fara batun a baya tana sakawa.
Ta ce ita ba ta daga cikin mutanen da ke da ra’ayin sanyawa da Sallah.
“Ba wai kudin ne bamu da shiba, kawai dai bamu da ra’ayi ne, wasu ma samarinsu za su roka su basu kuma a sanadiyyar haka sai a samu sabani a tsakani.
“Ga kuma wadanda suka ce za su yi bai kamata su takura kansu akai ba, akwai gumama da na gwanjo,” a cewarta
Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano
Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.
He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.
Hausa
Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December
Mukhtar Yahya Usman
The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.
Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.
He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.
“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.
The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.
Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano
Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”