Connect with us

Hausa

Shin za a iya fitar da zakkar fidda kai da kudi ko taliya?

Published

on

Farfesa Ahmad Murtala

Farfesa Ahmad Murtala

Bismillahir Rahmanir Rahim.

Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga Annanbinmu Muhammad da Alayensa da Sahabbansa bakidaya.

Bayan haka, a yau zan amsa tambayoyin da a ka dade ana tambaya wato halaccin fitar da kima a zakkar fidda-kai ko rashinsa. 

Tuntuni ban so na shiga amsa wannan tambayar. Sai dai tambayoyi kullum idan an zo karshen azumi, daf da Karamar, suna kara yawaita. A kan wannan tambaya aka rubuta wannan bayani. Allah ya bamu sa’a da dacewa.

1-Ana kiran wannan zakka da sunanye daban-daban. Daga ciki akwai ‘Zakatul Fidri’, wato zakkar da ake yi domin an kamala azumi za a koma cin abinci. Ana kuma kiranta da ‘Zakkatur Rikab’ “زكاة الرقاب”- (Al-Bayanu Wat Tahsil na Ibnu Rushd-Kakan:2/483). Fassarar da zata fi zama daidai da wannan ita ce ‘Zakkar Fidda-Kai’, duk da cewa an yi jam’i wuyaye a kalmomin laracin, amma fassarar Hausar ta fi zama daidai da wannan. Har ila yau, ana kiranta da ‘Zakatul Abdan’ “زكاة الأبدان” – wato zakkar da mutum zai fitarwa da kansa da kansa don ya tsarkaku.

2-Dalilai da yawa suna nuna wajibcin fitar da wannan zakka kamar hadisin Abdullahi bn Umar (R.A.) wanda ya ce, “Annabi (S.A.W.) ya farlanta fitar da zakkar fidda-kai sa’i guda na dabino, ko sa’i guda na sha’ir -(nau’in alkama ne)-, za a fitarwa da bawa da da, namiji da mace, karami da babba cikin Musulmi. Ya yi umarni da a fitar da ita kafin fitar mutane zuwa salla”-(Sahihul Bukhari, L:1503).

Haka nan a cikin hadisin Abu Sa’idil Khudri kuma ya ce, “Mun kasance muna fitar da zakkar fidda-kai sa’i guda na abinci-(an fassara shi da cewa yana nufin alkama)-ko sa’i guda na sha’ir ko sa’i gud.,,..,a na dabino ko sa’i guda na cukwi ko sa’i guda na busasshen inibi”-(Sahihu Muslim, L:2330).

Sa’i guda shi ne mudannabi hudu. Idan an yi la’akari za a ga sa’in zai yi daidai da kwano irin- na bogaji da ake amfani da shi a Kasar Hausa.

Wadannan hadisai, bayan nuni a kan wajibcin zakkar fidda-kai, sun bayyana irin abubbuwa da ake fitarwa da wannan zakka a lokacin Annabi (S.A.W) da Sahabbai. Hadisan sun nuna cewa ana fitarwa ne a kayan abinci guda biyar, wato: alkama, sha’ir, dabino, cukwi, busasshen inibi.

Ba bu wata ingatacciyar ruwaya da ta nuna Annabi yana fitar da kudi ko wani abin daban na kima ba abubuwan da aka ambata ba.

Wannan ya sa yawancin malamai suka tabbatar da cewa za a bayar da abinci ne kurum a wannan zakka. Domin yin hakan shi ne abin da nassin hadisan ya nuna baro-baro.

Aliyu bn abi uwais ya ce an tambayi Imamu Malik game da mutumin da yake wani wuri da ba abinci, shin zai fitarda zakkar fidda-kai da kudi!? Sai ya ce, A a wallahi! Sannan sai ya ce: mutum ya zamo a inda ba abinci, to shi me yake ci kenan!? Sai aka ce da shi ai ya zauna ne a wurin kamar wata daya, wata biyu!? Sai ya ce: idan ya dawo ya fitar da Zakkar fidda-kai din a abinci. Amma ba zai bayar da Wani abu ba abinci ba”-(Al-Amwal na Ibnu Zanjawaih, L:2456).

3-A daya bangaren akwai wani ra’ayin da yake ganin cewa za a iya bada kima ta adadin abin da za a fitarwa da zakkar.

Wani abu da yake da muhimmanci shi ne a san cewa wannan sabanin ra’ayi ba wai a wai zakkar fidda-kai kadai yake ba. Ya shafi har zakkar kudi da kayan noma da dabbobi. Amma akwai abubuwa guda biyu da yawancin masu tattauna wannan mas’ala ko karantata suke mantawa da su. Su ne:

i- Ra’ayin a bada kima ba wai sabon ra’ayi ba ne da aka kirkiroshi tsakanin duhun dare da sanyin safiya. Tsohuwar magana ce tun lokacin Tabi’ai akwaita.

ii- Ba malamin da yake ganin asali shi ne a bada kudi. Duk malaman da suke halatta a bayar da kima sun tabbatar da cewa bada abincin shi ne asali. Sai dai yanayin bukata da zai taso shi ne zai sa a koma ga zancen kima.

4- Mazahabin Malikiyya, wanda ake bi a wannan kasa, ya tabbatar da ana fitar da zakkar fidda-kai ne a abinci. Wannan ba wani sabani a kan haka. Sai dai ga wanda ya duba da kyau zai ga akwai rangwame da malaman mazahabin suke yi a cikin mas’alar, ta fuskar za a fitar da ita da wasu abubuwan na abinci ba wanda aka ambata a hadisin ba. Saboda suna da ma’ana daya da wadanda hadisan suka fada.-(Manahijut Tahsili na Arrajraji:2/455; Ikmalu Ikmalil Mu’lim na Ubbi:3/115, Kifayatid Dalibir Rabbani na Assazali:1/386-387). A wasu bayanan har da kudin ma kansu. Ga misalan irin wadannan bayanai daga cikinsu:

i-An tambayi Imamu Ibnul Kasim cewa, “Mutum ne ba shi da alkama a ranar da zai fitar da zakkar fidda-kai, sai yake son ya bawa mabukatan kudi don su saya da kansu, domin a ganin yin haka zai fi sauri? Sai Ibul Kasim ya ce, kada ya yi haka. Domin ba haka Annabi (S.A.W.) ya fada ba”. A wata ruwayar kuma sai Ibnul Kasim ya ce: Idan ya yi haka, ina ganin ba komai”.- Dangane da wannan ruwayar, Imamu Ibnu Rushd –Kakan, ya nuna cewa ba wani sabani tsakanin ruwayoyin guda biyun saboda ai ya basu kudin ne don su sayi alkamar su yi amfani da ita. – (Al-Bayan Wattahsil na Ibnu Rushd-Kakan:2/486-487; Annawadiru Waz Ziyadat na Ibnu Abi Zaid Al-Kairawani:2/303)

قال في العتبية:”وسئل-(ابن القاسم)- عن الرجل لا يكون عنده قمح يوم الفطر، فيريد أن يدفع ثمنه إلى المساكين يشترونه لأنفسهم، ويرى أن ذلك أعجل؛ قال لا يفعل ذلك. وليس كذلك قال رسول الله – صلى الله عليه وسلم. ومن رواية عيسى قال ابن القاسم: ولو فعل لم أر به بأساً.

قال محمد بن رشد الجد:”رواية عيسى هذه عن ابن القاسم، خلاف رواية أبي زيد عنه بعد هذا. وقد قيل إنها ليس بمخالفة لها. وإنما خفف ذلك في رواية عيسى هذه، لقوله يشترونه لأنفسهم، فإنما دفع الثمن إليهم على ذلك – والله أعلم، وبه التوفيق”.

Wannan ya nuna akwai rangwame a mas’alar, ba kaifi daya ba ce!

ii-Imamu Ash’hab yana ganin za a tsaya kurum a fitar da zakkar daga cikin wadannan kayan abinci da wadancan hadisai suka kawo. -(Ikdul Jawahirus Saminah na Ibnu Shash al-Khallal:1/219). Amma kunzumin malaman Mazahabin sun saba masa. Ta fuskar cewa za a fitarwa da abubwa har guda tara ko goma bisa duba da abincin da wasu garuruwa suke ci a lokacin da Imamu Malik ya bada fatawa.-(Mudawwanah: 1/391; Al-Bayan Wattahsil na Ibnu Rushd –Kakan:2/485). Sun kara: gero da dawa da shinkafa da Siltu da Alas. Wannan ya nuna a Malikiyyance ba bu laifi a fadada ma’anar hadisin zuwa ga duk abin da mutane suke ci a matsayin abinci. Wannan ta sa ma Imamu Ibnul Arabi Al-Maliki ya ce, “Ana fitar da zakkar fidda-kai ne daga abincin kowace al’umma. Masu shan nono su fitar a nono, masu cin nama su bayar da nama. Duk abin da suka ci, mabukatansu suna tare da su. Ba za su kallafawa kansu samo wani abin daban da ba su da shi su ba su ba, ba kuma zasu ki ba su abin da suke da shi ba”-(Aridatus Ahwazi na Ibnul Arabi Al-Malik:3/189; Ikdul Jawahirus Saminah na Ibnu Shash al-Khallal:1/219).

Sai dai yana da kyau a san cewa idan an ce abincin mutane gari ba ana nufin a tsahon shekara ba ne. Ana nufin irin abin da mutane suka rika ci a wannan watan na Ramalana kamar yadda Imamus Sawi ya fada.

Ya kara da cewa: Wannan shi ne zahirin abin da malamai irinsu Al-Haddab suka rinjayar. –(Hashiyatu Sawi Alas Sharhi Assagir:1/505)

 قال الصاوي-رحمه الله-:”والمنظور له غالب قوتهم في رمضان، على ما يظهر من الحطاب ترجيحه، لا في العام كله، ولا في يوم الوجوب”.

iii-Dangane da wadanda zasu fitar da kamar nono da nama da irinsu, sai malaman Malikiyya irinsu Imamu Abu Muhammad Abdullahi Asshabibi suka ce, “Sai a kaddara gwargwadon yadda sa’i guda zai ciyar, sai a bayar da kwatankwacinsa”. Duk da cewa akwai malaman da basu gamsu da wannan magana ba irinsu Al-Burzuli, amma wasu manyan malaman Malikiyyar irinsu Imamu Al-Haddab suna nuna wannan magana tana da karfi. Haka nan Al-Khirshi.-(Mawahibul Jalil na Al-Haddab: ; Sharhul Mukhtasar na Al-Khirshi:1/229; Sharhul-Izziyyah na Azzurkani: sh/482).

iii-Imamu Malik yana ganin baure-التين-ba abinci ba ne don haka ba za a bayr da zakka ta kayan abinci ko zakkar fidda-kai da shi ba. Amma sai Malaman Mazahabin tun daga kan Ibnul Kasim da Abdulmalik bn Habib da Abubakar Al-Abhari, da malaman Bagdada irinsu Isma’ilu Alkadi, da malaman Andalus (Spain) irinsu Al-Baji da Ibnu Abdilbarri suna ganin za a iya bayarwa ga wadanda bauren abinci ne a wurinsu. Imamul Baji ya ce, “Abin da yake mafi daidai a wurina shi ne baure nau’i ne na abinci. Don haka za a fitar masa da zakka, riba kuma zata iya shiga cinikayyar da shi, wadanda suke cinsa za su iya fitar masa da zakkar fidda-kai”- .-(Al-Muntaka na Baji:2/171; Al-Kafir na Ibnu Abdilbarri: sh/100; da Al-Jami’u Li Ahkamil Kur’an na Kurdubi: 7/103).

قال الإمام الباجي:”والصواب عندي أنه من الأقوات وأن تجزئ فيه الزكاة والربا ويخرجه في زكاة الفطر من يتقوته”.

A zamanin yanzu zamu dauki wannan ruhusar a kan kayan abinci da suka shafi taliya da macaroni da indomine da sauransu, cewa a kimanta abin da zai iya isa kwano daya a bayar.

vi- Duk da an ruwaito cewa shi Imamu Malik ba ya ganin za a fitar da zakkar fidda-kai a gari, amma wasu daga cikin malaman Mazahabin Malikiyyar kamar irin su Ibnu Habib da Asbag da sauransu suna ganin za a iya fitar da gari wanda zai daidai da sa’i guda.-(Ikdul Jawahirus Saminah na Ibnu Shash al-Khallal:1/219). Ma’anar wannan maganar tasu shi ne wanda yake da garin samovita da ko garin fulawa da sauran irinsu zai iya fitar da su a matsayin fidda-kai.

v-Imamus Sawi, daya daga cikin hamshakan malaman Mazahabin Malikiyya na daga baya, ya duba wannan mas’ala da idon basira sai ya yi bayanai da suke dada tabbatar da halascin a karbi kima. A daidai inda ake cewa sai wadannan kayan abinci guda tara ko goma ne kurum za a fitarwa da zakka, sai ya ce, “Amma magana mafi bayyana ita ce idan an bayar da kudi zakkar ta yi. Saboda ana samun toshe bukatar mabukaci a wannan rana da kudin”. -(Bulgatus Saliki na Assawi:1/438)

قال الصاوي:”فالأظهر الإجزاء لأنه يسهل بالعين سدّ خلته في ذلك اليوم”

5- Wadansu hadisai sun bayyana hikimar shar’anta wannan zakka ta fidda-kai shi ne tausasawa mabukata da wadatasu ga barin yin roko a wannan rana. Abdullahi bn Abbas ya ruwaito cewa Manzon Allah ya farlanta fitar da zakkar fidda-kai don tsarkake mai azumi daga siriri da maganganun batsa. Sannan kuma don ciyarwa ga maiskinai (mabukata).

Wanda ya bayar da ita kafin sallar idi, to an karba. Wanda kuwa ya bayar da ita bayan sallar idi, to ta zamo sadaka kurum kamar sauran sadkoki”-(Abu Dawud, L:408)

Wannan hadisin ya bayyana alfanu guda biyu da za a samu ta hanyar yin zakkar fidda-kai. Shi mai azumi a tsakakeshi. Su kuma mabukata a yalwata musu a wannan lokaci. Don haka ciyar da mabukatan wata babbar manufa ce.

Annabi (S.A.W) ya nuna a bayar da abinci shi ne asali. A zahiri kuma idan ciyarwar zata zamo sai dai a basu kudin su nemi abinci su saya, shi ma ya yi.

Idan an yi la’akari, akwai kasashe irin na Turai da za a ga samun zallar kayan abinci irinsu alkama da gero da dawa da sauransu yana da wahala ga mazauna birane, irin wadannan ba laifi suma su bayar da kudade ko wata kima.

6- Bayar da kima ko canza wani abu da wani abu da zai fi alfanu a irin wadannan hidimomi na al’umma ba wai wani sabon abu ba ne. Domin ga ruwayar da Mu’azu bn Jabal ya je Yaman karbar zakka ko jiziya -kamar yadda Dawus bn Kaisana ya ruwaito daga wurinsa, yana cewa da mutane Yaman, “Ku bani yadi ko gwado a maimakon sha’iri da gero. Wannan zai fiye muku saukin bayarwa. Sannan kuma sahabban Annabi (S.A.W.) a Madina zasu fi son haka”-(Bukhari ya kawo shi a Ta’aliki. Dawus bai hadu da Mu’azu ba. Duba Fat’hul Bari:3/311).

Imamul Bukhari da wasu malaman suna kafa hujja da wannan ruwaya a kan halascin a duba masalaha wajen fitar da asali kayan abinci ko kuma kima.-(Al-Majmu’u na Nawawi:5/429; Fat’hul Bari na Ibnu Hajar:3/312).

Ibnu Habib daga cikin manyan malaman Malikiyya na farko ya bada fatawa irin wannan dangane da wanda zai bada zakkar kudi, sai ya ga abinci ya fiyewa mutanen da za a bawa. Ya ce sai ya basu abinci a maimakon kudin. Ya kara da cewa, “Ya fitar a kayan abinci domin saukakawa mabukata a lokacin da mutane suke da bukatar abincin. Idan ya zamo yana wahala, ba a samunsa da sauki-(Al-Bayan Wat Tahsil na Ibnu Rushd-kakan:2/512)

قال ابن حبيب:”…أن يجب عليه عين فيخرج حبا-إرادة الرفق بالمساكين عند حاجة الناس إلى الطعام، إذا كان عزيزا غير موجود”.

7-A cikin hadisin da Sayyadin Abubakar ya bayyana yadda nisabin zakka yake na kudi da na kayan noma da ya zo na dabbobi sai ya ce, “Wanda zakkarsa take ya bayar da rakuma ‘yar shekara biyu amma ba shi da ita, sai dai yana da ‘yar shekara uku, to za a karba. Sai kuma mai sa’i (wakilin gwamnati a karbar zakkar) ya bashi dirhami ishirin ko akuyoyi guda biyu”.-(Bukhari:3/311-312-Fat’hul Bari).

Idan an yi la’akari za a ga an halatta bada kima a nan. Shi ya sa wasu hamshakan malamai irinsu Abu Ubaid suka ce ba laifi idan bukatar bada kima ya taso a bayar koda kuwa a ainihin zakka ne ma baki daya. –(Al-Amwal na Abu Ubaid:sh/458).

Idan an bayar a babbar zakka, to ina ga zakkar fidda-kai!

8-Manyan malaman Mazahabin Malikiyya irisnu Ibnu Abi Hazim da Muhammaad bn Dinar da Ibnu Wahad da Asbag suna ganin da mutum zai yi gaban kansa ya fitar da zakka maimakon ya bayar da kayan abinci ko dabbobi (a babbar zakka fa kenan), sai ya bayar da kudi, suka ce ya isar masa. Duk da dai ba a so ya yi hakan ba tun farko. Ibnu Rushd-Kakan ya karfafi wannan magana da cewa it ace magana mafi bayyana.-(Hashiyatud Dasuki:1/499 da 502; Hashiyatur Rahuni Ala Sharhil Mukhtasar:2/324-330; Ikdul Jauharil Samin na Ibnu Shad: sh/85).

9- Idan muka duba sauran malamai masu wannan ra’ayi na fitar da kima da kudi a zakkar fidda-kai zamu ga akwai Manyan Tabi’ai irinsu Hasanul Basari da Umar bn Abdul’aziz da Abu Is’haka Assabi’i da sauransu da suke da ra’ayin. Ga kadan daga cikin bayanansu:

i-Daga Hasanul Basari ya ce, “Idan mutum ya bayar da kudi (dirhami) a zakkar fidda-kai, ya isar masa”-(Al-Amwal na Humaidu bn Zanjawaih, L:2454)

عن الحسن قال:”إذا أعطى الدرهم من زكاة الفطر أجزأ عنه”

ii-Abu Is’haka Assabi’i ya ce, “Na riskesu (yana nufin Sahabbai da Tabi’ai) suna bayar da kudi a kimar abinci a zakkar fidda-kai”-(Musannafu Ibnu Asi Shaibah:3/174).

10-A Mazahabin Abu Hanifa da Imamu Sauri da Is’haka bn Rahawaihi da sauransu duk suna halatta bada kima. Ba wai a zakkar fidda-kai kawai ba. A duk abin da ya shafi kaffara da bakance da sauransu.-(Al-Mabsud na Assarkhasi:3/113-114; Umdatul Kari na Al-Aini:9/8)

 A dunkule, fitar da abinci shi ne asali. Kuma mutum ya yi kokari ya duba mutane da suke da bukatar abincin ya basu. Amma idan kuma ya yi la’akari da bukatar bada kima da kudi sai ya bayar a inda ake da matsananciyar bukatar hakan. Shehul Islam Ibnu Taimaiyya ya yi bayani irin wannan hali da cewa, “Ya halatta a fitar da kima a zakka a inda ba za a iya kaucewa bukata da masalahar yin hakan ba. Kamar a ce ya sayar da kayan gonarsa, a irin wannan hali sai ya bayar da dirhami goma ya isheshi. Ba sai an dora masa nauyin sai ya sayo kayan noman ko alkamar ba domin ya riga ya tallafawa mabukacin da kansa. Imamu Ahmad bn Hanbal ma ya fada halascin yin hakan baro-baro. Wani misalin kuma a ce akuya zai bayar a zakkar shanu, amma ba shi da akuya. A nan fitar da kimar ya wadatar da shi, ba sai an kallafa masa ya tafi sayo akuyar ba. Ko kuma su wadanda suka cancaci a basu zakkar su nemi a basu kimar su da kansu saboda ta fiye musu. Wannan ma ya halatta”-(Majmu’ul Fatawa na Ibnu Taimiyyah:25/82-83; Al-Ikhtiyaratul Fikihiyya na Ibnul Lahham: sh/103)

Allah ya bamu sa’a da dacewa a duniya da Lahira.

Farfesa Ahmad Murtala, shi ne shugaban Sashen Nazarin Ilimin Addinin Musulunci na Jami’ar Bayero dake Kano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Trending