Connect with us

Hausa

Sheikh Abduljabbar ya kuma korar lauyoyin da suke kare shi a Kotu

Published

on

Nasiru Yusuf

A karo na biyu Sheikh Abduljabbar ya kuma korar lauyoyin da suke kare shi a Kotu, inda yake ake tuhumarsa da yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW).

A zaman kotun na ranar Alhamis, Sheikh Abduljabbar ya fadawa Kotu cewa lauyoyinsa sun gaza kare shi, don haka shi ne zai cigaba da kare kan sa.

Malamin ya ce ya yarda da duk shawarar da Alkali ya ba shi na kada ya cire lauyoyinsa daga cikin shari’ar,

Abduljabbar ya ce tun asali lauyoyinsa ne suka hana shi ya yi magana har aka kai shi Asibitin duba kwakwalwa, kuma suka rika tsorata shi da cewar za a yanke masa hukuncin kisa domin angama komai da su lokaci kawai ake jira.

A cewar Malamin wannan ne yasa har ya kawo yanzu yana gidan kaso.

Malamin ya kuma zargi lauyoyinsa na baya da keta alfarmar iyalinsa, wanda ya ce bai ji dadin hakan ba.

“Amma nasan duk lauyoyin nan ba za su iya kare ni ba. Idan kuma na kyale su, to zan iya zubar da mutuncina, ko ba komai. Don haka ni abun da nake so in ce, wannan rigima duk akan auren Nana Safiyya ne da kuma maganganun da ake cewa na ce, duk ina da abun da zan fada, domin haka, ko mun zauna da lauyoyina ko bamu zauna da su ba, ba za su iya baiyana wadannan hujjojin nawa ba. Domin ba lauyan da yake Jin Arabiyya a cikin su.

“Don haka magana ta gaskiya ni sharia  ta da ake tuhumata ba ta ‘law’ ba ce ta Hadisai ce.  Kuma ni ne nasan Hadisan su lauyoyi ba su san su ba. Domin lauyana na baya da ya kafe na ba shi hujjojin, amma bai iya bayar da su ba a gaban kotu. Sai ya ce in bashi duk hujjojin, don ya cuda su a cikin ‘law’ amma bai iya yin hakan ba.

“A karshe sai suka ce shi shaida na farko jahiline.  Shi ne na ce, ta ya ya za a yi jahili ya haddace Alqur’ani da hadisi littafi ashirin, fa fiqihu goma, ku ce masa jahili?  Kuma nace musu ga bayanina a mp3 su danna kowa ya ji. Sai suka ce shi shaida bai danna komai ba,” A cewar Sheikh Abduljabbar.

Sheikh Abduljabbar ya ce ya ba wa lauyoyinsa samina akan ga yanda za su yi, amma sun kasa kare shi, don haka ya yanke shawarar shi zai iya kare kansa.

Sannan ya shaidawa Kotu daga yanzu ya cire duk lauyoyin da suke kare shi a cikin wannan shari’a da ake yi.

Malamin ya gabatarwa da Kotu bukatar ta ba shi dama ya yi wa shaida duk tambayar da ya tsara.

Sai dai lauyan gwamnati ya ki amincewa da abun da Sheikh Abduljabbar ya nema, inda yace a doka ba a yin irin wannan shari’a babu lauya domin idan fa abinda ake tuhumar malamin da aikatawa ya tabbata to hukuncin kisa ne akan shi.

Don haka ya ce bai yarda Sheikh Abduljabbar ya cire lauyoyinsa ba, amma zai iya yi wa shaida duk tambayoyin da yake so.

Sannan ya roki kotu ta ba wa Sheikh Abduljabbar dama ya je ya yi nazari, su ma lauyoyinsa su yi nazari, kuma su ma lauyoyin gwamnati su yi nazari sannan a cigaba da shari’a.

Daga bisani Kotu ta gamsu da wannan rokon na lauyan gwamnati dan gudun yin kuskure a cikin sharia.

Alkali ya waiwayi Sheikh Abduljabbar ko ka yarda a daga sharia zuwa wani lokaci, ya ce ya yarda.

Da Alkali ya tuntu6i lauyoyin Sheikh Abduljabbar, sai lauya Umar Faruk ya ce, sun san halin da Sheikh Abduljabbar yake ciki, don haka suka ba shi dama ya yi magana da kan sa.

Lauya Umar Faruk ya ce, duk da malamin ya ce, ya ciremu to mun yarda da abun da Kotu ta fada na a daga sharia kuma muna cikin wannan shari’ar daga nan har ta kare domin muna tausayamasa halin da yake ciki amma shi bai san abun da mu muka sani ba shi yasa. Yana cikin gaggawa ne. Kuma a fagen irin na sharia ba fagen a bude littafi a koyar da karatu ba ne.  Fage ne na ilimin sharia, don haka muna yi masa uzuri.

Alkali ya kara Jan hankalin lauyoyin Sheikh Abduljabbar da suyi hakuri akan kalaman malamin kuma kada su janye su cigaba da hakuri da tattaunawa.

Daga nan Alkali ya daga cigaba da zaman shari’ar zuwa ranar Alhamis 11 ga watan Nuwamba, 2021.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending