Connect with us

Hausa

Siyasar da za a yi a Kano 2021-2023

Published

on

Malam Ibrahim Shekarau da Engr. Rabiu Musa Kwankwaso

Bello Muhammad Sharada

Tun a bara a watan Disamba na sha alwashin zan yi rubutu da  lakabi na sama. Abubuwa da yawa sun faru har suka kawo wannan jinkiri, YAU ga shi zan sauke wannan nauyin cikin yardar Allah.

A Disambar da ta gabata na kudurce magana ne akan yadda za ta kasance a Kano, bayan na yi nazarin yadda aka gudanar da zabukan ciyamomi na APC. Cikin ikon Allah kuma a jiya da daddare Alhaji Murtala Sule Garo, kwamishinan kananan hukumomin na jihar Kano ya sulale bayan kowa ya watse ya jagoranci ciyamomi na kananan hukumomi 44 ya ziyarci gidan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso domin yi masa ta’aziyya na mutuwar kaninsa shakiki Muhammad Inuwa.

Domin mu sani wadannan ciyamomi sune wanda Hajiya Gwaggo uwar Kanawa da Alhaji Murtala Sule Garo da Alhaji Abdullahi Abbas suka dora akan mulki watanni 11 da suka shude. Haka kuma sune wakilai da ake zato za su yi wa Kwamanda aiki a takarar gwamnan Kano ta 2022-2023 a bisa tsarin Farfesa Hafsat Ganduje, mai dakin gwamna Ganduje.

Wannan ta’aziyya rokon iri ce. Sharar fage ne. Sake lissafi ne. Ni haka na fassara ta. Abin da na fahimta an tara ‘yan tamore, masu yin siyasa bukata, masu yin siyasar kwadayi. Rakuma da akala.

Sai dai irin wannan yanayin a gurina abin farin ciki ne Kwankwaso ya bada auren ‘yar Shekarau. Abin dadi ne Ganduje ya je har gida ya yi wa Kwankwaso ta’aziyya. Gungun yan Gandujiyya su yi takakkiya gaishe da madugu.

Babban kuma farin ciki shi ne, za a daina fadan siyasa na matasa. Za a sassauta jagaliya a fili da rediyo da New Media. Magoya baya zasu rage tsawo na so da kiyayya. Za a koma kan gundarin siyasar manufa da akida da ‘yanci, a wurgar da tumasancin siyasa da biyan bukata.

A tsawon shekara shida zuwa bakwai na mulkin Baba Ganduje kowa zai ba shi shaidar yana zuwa gaisuwar mutuwa da jana’iza da dubiyar maras lafiya da jaje da shi da matarsa, kuma komai kankantar gudunmawa in ta taso zai bayar.

Ba a taba yin gwamna a Kano da ya samu kuri’ar cin zabe ba irinta Ganduje. Ya samu kuri’ar sama da miliyan daya da rabi a zabensa na 2015. Sannan shi ne kadai da ya yi gwamna karo na biyu tare da goyon bayan kowane tsagin siyasa in banda Kwankwasiyya. Sai da ya shawo kan kowa ya bi shi. Amma ba wani gwamna da ya tara bakin jini da hamayya a Kano kamarsa. A tsawon mulkinsa abu guda biyu ya yi wadanda suka jawo masa son barka. Na farko ya cire Sarkin Kano Halifa Muhammad Sanusi II ya kafa sabbin masarautu guda biyar. Na biyu ya dauki mataki akan Sheikh AbdulJabbar Nasir Kabara.

Sai dai kuma faifan bidiyon da aka yada yana cusa Dala a cikin aljihunsa da dan cikinsa da ya kai shi kara EFCC da shigar matarsa dumu-dumu da karfin ikon da take da shi a kowacce harka ta mulkinsa da sakarwa Murtala Sule Garo da Abdullahi Abbas kowacce sabga ta jam’iyyar APC da dora marasa kwarewa a madafun iko, sannan duk harkar kasuwanci da walwala da tausayi da aikin gwamnati da muwalatin ‘yan siyasa babu wata kulawa. Uwa-uba kuma babu wani mai girma da daraja da dattaku a Kano, kowa banza ne, ga kuma musibar tattalin arziki da tsaro su suka dada dagula shirin gwamna Ganduje.

Kanawa bamu da jiha sama da Kano. Duk balokokon da nake yi da masu irin ra’ayina, muna yi ne, don ta bunkasa, tsarin ya amfani al’umma, kuma dukiyar da aka baiwa Kano a yi amfani da su ta hanya mai kyau.

Ina sha’awar jihar Kano ta zama zakara akan sauran jihohi ta fuskokin rayuwa, ina so a rika buga misali da Kano a cikin alheri, ina son Kano ta zama abin koyi da kwatance a cikin sauran takwarorinta. Muna jin labarin jihohi a duniya kamar Selangor a Malaysia da California a America da Taiwan a China da Madina a Saudi Arabia. Haka muke son a ce Kano a Najeriya.

Idan Allah ya nufa nan da watanni takwas za a fitar da wanda zai gajeka a Kano. Cikin watanni masu zuwa hayaniyar siyasa da karbar madafun iko shi ne zai mamaye komai. A shekara 22 da dawowar mulkin farar hula a wannan jamhuriya, da kai aka yi komai. Ka zarce sittin, yanzu ka haura 70, ka doshi 80,  ka san komai kuma ka ga komai. A  cikin shekara 22 ka nuna kwarewar ka a likimo, kai gwani ne.

Bari mu dan yi ratse, mu waiwaya baya. Bayan faduwar PDP a zaben 2015, an rubuta littafai manya da suka shafi siyasar jam’iyyar PDP da mulkin Goodluck Ebele Jonathan. An yi tsokaci kan sababin da ya kawo faduwar PDP bayan shekara goma sha shida a mulki. Na karanta littafai hudu, da suka hada da Against the run of play na Olusegun Adeniyi 2017 da On A Platter of Gold

na Bolaji Abdullah 2018 da My Transition Hours na Goodluck Ebele Jonathan 2018 da Burden of Service na Mohammed Bello Adoke 2019, in ka cire wanda Jonathan ya rubuta da kansa, kaf dinsu sun dangata rawar da mai dakin Jonathan Madam Patience ta taka ya jawo faduwar GEJ/PDP. Matsalar Ganduje bayan ta ‘yan Kwankwasiyya ta Goggo ita ce ta biyu.

 A bana lissafin siyasar Kano sabo ne fil kuma salone da zai zo ba a san irinsa ba a baya. Za a ga abubuwa na siyasa na daban. Idan lokacin ya kara fadada kada a yi mamaki. An samu juyin bukata da yanayi.

Zabi biyu ne da masu lura da sha’anin siyasar gwamnatin tarayya  a Kano suke da shi. Bukatarsu ita ce su samu kuri’a mai kauri daga Kano kowa ye ma zai zama gwamna ruwansu. Zaben shugaban kasa da majalisun tarayya shi za a fara yi.

Zabin kuwa sune ko dai su saka baki bangaren G7 su karbi ragamar Kano su tankade Ganduje can, as-as haihata-haihata, sannan su lallaba su jawo Kwankwaso a hadu guri guda, ko kuma a  watsawa G7 kasa a ido a tabbatar da duk wani tsari da gwamna Ganduje ya zo da shi.

Menene babbar bukatar Kwankwaso? Yana son zama shugaban kasa ko mataimakin shugaban kasa ko ministan Abuja. Sannan yana son wanda duk zai zama gwamnan Kano daga Kwankwasiyya zai fito. Mecece bukatar Ganduje da Goggo, su dora gwamna da zai rufa musu asiri da kare mutuncinsu in sun bar gidan gwamnati, daya daga cikin ‘ya’yan Ganduje ya samu zababben kujera, shi kansa ko ya zama mataimakin shugaban kasa ko Sanatan Kano ta arewa, matarsa kuma ta zama Sanata daga Jigawa.

Mecece bukatar ‘yan G7 shin Barau I. Jibrin ko Sha’aban Ibrahim Sharada ko Shehu Dalhatu ya zama gwamna? Shekarau ya koma Sanatan Kano ta Tsakiya? Abduwa da Dederi da Jobe su koma kan kujerunsu?. Wannan ba ita ce manufar da ya kamata mu dora tunani na al’umma a kai ba. Yanzu burin da ya zamar mana wajibi shi ne; ceto Kano ta zama ta mutanen Kano, harkokin siyasar Kano su kasance a doron dimokuradiyya da ‘yanci da ci gaba da mutunci da zaman lafiya. Babban aikin da za a sanya a gaba shi ne bukatar yadda za a farfado da Kano ta koma matsayinta na asali har ta  zarce kowa a kasuwanci da ilimi da sana’a da fasaha da sarauta da addini da al’ada da lumana da zaman lafiya. A rinka alfahari da ita a duniya.

Wannan burin ya fi karfin Kwankwaso da Kwankwasiyyarsa. Ya fi karfin Shekarau da Mundubuwarsa, burine na dindindin domin Kanawa da Najeriya.

Bello Muhammad Sharada

Shi ne Sakataren dake kula da walwalar ‘Yan Jam’iyyar APC (State Welfare Secretary) na Jiha tsagen Ahmadu Haruna Zago.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Hausa

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero, Baƙon Shehu Maghili

Published

on

Magaji Galadima

 

 

A ranar Litinin 12 ga watan Disamba 2022 gwamnatin ƙasar Aljeriya ta aiko da wani jirgi na musamman domin ya ɗauki mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero zuwa ƙasar ta Aljeriya domin halartar taron duniya na musamman don tunawa da rayuwa da kuma aiyukan shahararren malamin addinin Musulunci sharifi kuma masanin falsafa  wato Shehun malami Muhammad Abdurrahman al-Maghili wanda yayi rayuwarsa tun a ƙarni na goma sha biyar. 

Jigin ya tashi daga Kano da karfe 9:45 na safe. A cikin waɗanda suka samu alfarmar raka Sarki wannan tafiya akwai Sarkin Dawakin Tsakar-gidan Kano Alhaji Ahmad Ado Bayero hakimin Kumbotso da Ambasada Ahmad Umar Ɗanmalikin Kano da Dakta Ibrahim Ɗahiru Bauchi wanda ya wakilci Sheikh Ɗahiru Bauchi da Malam Isa Sanusi Bayero da Dakta Lawi Atiku Sanka da kuma ni Magaji Galadima Kachallan Kano, sannan sai wasu malamai da sharifai na Kano da kuma fadawa hadiman Sarki.

Jirgin ya ɗan yada zango a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar inda ya ɗauki Sultan na Agadas da Sarkin Sharifan ƙasar Nijar da sauran malamai da muƙaddamai da malaman jami’a. Sarkin Kano da ‘yan tawagarsa sun sauka a Aljiyas babban birnin Aljeriya da misalin karfe 5:00 na yamma inda manyan ministoci da jami’an gwamnati dana diflomasiyya da kuma manyan malamai suka taryi mai martaba Sarki da tawagarsa. Daga nan akayi jerin-gwano aka raka Sarki masaukinsa.

A rana ta biyu wato Talata Sarki da ‘yan tawagarsa suka fita zuwa wajen taron ƙasa da ƙasa da aka shirya domin tunawa da shahararren malamin addinin musulunci masanin falsafa kuma sharifi wato Shehu Muhammad Abdurrahman al-Maghili wanda yayi rayuwarsa tun a ƙarni na sha biyar kuma har ya zo Kano zamanin Sarki Muhammadu Rumfa.

Al-Maghili ya zauna a Kano tsawon lokaci kuma ya bijiro da sababbin tsare-tsare ma su muhimmanci a fadar Kano, kana kuma ya yi rubuce-rubuce akan ibada da hukunci, sannan ya rubuta wani kundi da ya zama daftari na jagorar duk wani sarki na Kano da ma nahiyar yammacin Sudan.

Taron an shirya shi ne a babban ɗakin taro na ƙasar dake birnin Aljiyes.  A ranar buɗe taron Sarkin Kano da tawagarsa sun isa wajen da misalin karfe 9;00 na safe amma sai aka kaishi wani ɗaki ya zauna a kauwame har sai da ɗakin taron yayi cikar kwari sannan aka shigar dashi.

Toh dama an ɗauki makwanni ana ta yaɗawa a kafafen labarai cewa ƙasar ta Aljeriya zata karɓi bakuncin wani ƙasaitaccen Sarki mai alfarma da daraja daga garin Kano a Nijeriya, don haka mutanen ƙasar duk sun zaku suga wannan ƙasaitaccen Sarki. Saboda da haka yana shiga ɗakin taron sai duk aka tashi tsaye waje ya kaure da sowa da tafi, mata kuma na rabka guɗa, su kuma ‘yan badujala suka goce da wani irin take na musamman da ake kaɗawa mashahuran mutane in sun shigo wajen taro.

An ɗauki tsawon lokaci kafin a samu natsuwa lamurra su koma daidai sannan mai martaba Sarkin Kano figinai suka yi sayi ya zauna aka gyara aka kimtsa sannan aka fara gudanar da taro.

Daganan ne kuma sai aka fara jawabai, babban ministan harkokin addini na ƙasar shine ya wakilci shugaban ƙasa kuma yayi jawabin maraba ga mahalarta taron kana yayi godiya ta musamman ga Sarki Aminu Bayero a madadin shugaban ƙasa da al’ummar ƙasar baki ɗaya. Shima Sarkin na Kano  yayi jawabi inda ya nuna farin ciki da godiya ga gwamnati da jama’ar ƙasar baki ɗaya saboda kyakkawar taryar da aka yi masa, ya kuma isar da gaisuwar jama’ar masarautar Kano da Nijeriya baki ɗaya a garesu.

Sarkin ya yaba da hangen nesan waɗanda suka assasa wannan taro na tunawa da Shehu Maghili wanda yace yafi cancanta a kira shi da Bakano maimakon dan Aljeriya saboda da dalilai da dama. Ya baiyanawa mahalarta taron cewa a yanzu haka a cikin birnin Kano akwai unguwar Sharifai waɗanda asali jama’ar da suka zo Kano tare da Shehu Maghili sune ke zaune a wannan unguwa tun lokacin har zuwa yanzu, kuma shugabansu Sidi Fari shine Sarkin Sharifan Kano kuma yana da gurbin zama a majalisar Sarkin Kano.

A ƙarshen jawabin Sarki yayi godiya ga Allah wanda Ya ƙudura cewa a zamaninsa ne akayi wannan babbar hobbasa ta sake dawo da wannan tsohuwar alaƙa tsakanin Kano da Nijeriya da kuma ƙasar Aljeriya kamar yadda su Shehu Maghili suka shimfiɗa.

Daga nan kuma sai aka buɗe fage inda malamai da masana suka yita ƙwami akan tarihin rayuwa da rubuce-rubucen Shehu Maghili.

Bayan an tashi daga taron wannan rana ta farko, sai mutane suka yanyame Sarkin Kano, malamai da jami’an gwamnati da baƙi daga sauran ƙasashe kowa burinsa shine ya samu ya ɗauki hoto da Sarkin Kano.

Bayan an fito waje ma haka har zuwa inda ya shiga mota. Mu ma ‘yan kwarakar Sarki da kyar muka yakice ‘yan jarida masu son jin kwakwaf domin yawansu babu lokaci da zamu warware musu zare da abawa. Koda muka isa masauki sai muka tarar ashe tuni wasu jama’ar sun yi kwamba suna jiran isowar Sarki domin su samu su gaisa kuma su ɗauki hoto da shi.

 

Bayan ya shiga ɗaki kuma sai manyan malaman ƙasar su kuma suka yi layin shiga suna yiwa sarki addu’a har saida rana tayi gora sannan jami’an tsaro suka tare mutane suka hana su shiga don a kyale Sarki ya huta.

A rana ta biyu mai martaba Sarki da tawagarsa ya sake komawa wajen taron inda malamai suka ci gaba da gabatar da takardu.

Bayan anyi hutun zango na farko sai mai martaba Sarki ya fita domin kai ziyara ofishin jakadancin Nijeriya dake kasar ta Aljeriya.

Jakadiyar Nijeriya Hajiya Aisha Muhammad Garba ta taryi Sarki da tawagarsa kuma anyi jawabai masu muhimmanci.

Da maraice kuma har ila yau sai Jakadiyar ta shiryawa mai martaba sarki wata liyafar alfarma a gidanta inda aka gaiyaci ‘yan Nijeriya mazauna ƙasar Aljeriya da kuma wasu malamai daga Nijeriya.

A rana ta uku kuwa mai martaba Sarki ya halarci bikin rufe taron kuma abin ya ƙayatar ƙwarai musamman yadda Sarkin Kanon ya zama tauraro a wajen taron domin dai hankalin kowa na kansa tun daga farko har i zuwa lokacin da aka ja labulen rufe taron.

Da yammaci kuma sai shugaban ƙasar Aljeriya Abdelmadjid Tebboune ya gaiyaci Sarki Aminu zuwa fadarsa inda suka zauna suka yi zantuka na girma. Shugaban ƙasar yace yayi murna matuƙa da karɓar baƙuncin Sarkin, ya ƙara da cewa gwamnatin ƙasar tasu tana sane da tarihin masarautar Kano da rawar da Shehu Maghili ya taka wajen bunƙasa al’adu da addinin Musulunci a birnin Kano.

Shugaba Tebboune yace Sarkin Kano a wannan ziyara shi baƙon Shehu Maghili ne, duk da yayi wafati fiye da shekaru 600, wannan ziyara ta Sarki lallai Shehu Maghili shine sila.

Shi kuma a lokacin da yake maishe da jawabi Sarki Aminu yayi godiya ga Allah da Ya bashi ikon amsa gaiyatar shugaban ƙasar da kawo wannan ziyara, ya yabawa gwamnatin ƙasar Aljeriya saboda ɗawainiyar ɗaukar nauyin wannan taro mai muhimmanci.

Daga nan kuma sai yayi kira ga shugaban na Aljeriya da su haɗu su farfaɗo da hulɗar cinikayya da kasuwanci tsakanin Kano da Aljeriya wanda yace zai taimaka wajen ƙara yauƙaƙa danƙon zumunci tsakanin nahiyoyin biyu. Baya ga wannan kuma da yake ance lokacin iska ake cin ɗan jinjimi sarkin ya bukaci gwamnatin ƙasar ta Aljeriya da ta bawa ɗaliban jihar Kano tallafi na guraben ƙara ilmi a fannoni dabam-daban a jami’oin ƙasar inda shugaban ƙasar nan take yayi wuf yace ya amince da wannan shawara kuma yana jira in Sarki ya koma gida,  ya tsaro jadawalin yadda duk yake so ayi , su kuma in Allah Yaso zasu aiwatar. a nan dai akayi muwafuƙa duk shawarar tasu tazo daidai.

Daga nan suka yi bankwana cikin farin ciki da girmama juna.

A rana ta hudu mai martaba Sarkin Kano tare da wasu daga cikin ‘yan tawagarsa sun ziyarci garin Ain-Madhi wato ainihin garin da aka haifi Maulana Shehi Ahmadu Tijjani (RA) wanda ya kafa ɗarikar Tijjaniyya.

Sarkin ya ziyarci muhimman wuraren tarihi a garin sannan ya gana da manyan malamai da sharifai zuriyar Shehin inda suka yiwa Sarkin da Kano da Nijeriya  addu’oi na musamman.

A rana ta biyar Sarki ya kammala ziyarar kamar yadda aka tsara, don haka sai ya karyo linzami zuwa gida. Manyan jami’an gwamnati da malamai da kusoshin diflomasiyya da kuma jakadiyar Nijeriya sune suka raka mai martaba Sarki zuwa filin jirgin sama, akayi ban kwana kowa na cike da farin ciki.

Ko shakka babu wannan ziyara da mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Bayero ya kai jamhuriyyar dimokuraɗiyyar ƙasar Aljeriya ta buɗe wani sabon babi na dangantaka mai ƙarfi tsakanin ƙasar da kuma Nijeriya. Wannan tagomashi da Sarkin Kano yake samu a duk inda yaje lallai abin godiya ga Allah ne ga duk mai ƙaunar ci gaban jihar Kano da Nijeriya baki ɗaya.

Ɗadin daɗawa gashi har mai martaba Sarki yayi hobbasa har shugaban ƙasar na Aljeriya yayi alkawarin baiwa ɗaliban jihar Kano guraben ƙaro ilmin jami’a kyauta da shiryawa malamai da limamai kwasa-kwasai na ƙara sanin makamar aiki, sannan a waje ɗaya kuma shugaban na Aljeriya ya bada umarni cewa ayi duk abinda za ayi don ganin kwance duk wani daurin Gwarmai don sassauta hulɗar kasuwanci ga ‘yan kasuwar Nijeriya masu sha’awar zuwa Aljeriya.

Mai martaba Sarki ya samo nasarar da ba a taɓa samowa ba a bigiren dangantakar  siyasa ko diflomasiyya, don haka babu abin yi da ya wuce mu yiwa Allah godiya da muka samu Sarki wanda addu’ar magabata da kyakkawar mu’amala  da nagartaccen lamiri suke haskaka masa turbar tafiyarsa, ba kuskunda ba jalla-kujalle.

Fatanmu shine Allah Mabuwayi Ya kara wa Sarki lafiya da jimiri da jinkiri, yadda yake fafutukar samawa al’ummar Kano tudun dafawa, shima Allah Ka dafa masa.

Yadda Sarki ya ɗauko saitin gwadabe tun ba a je ko’ina ba a tafiyar yayi nuni da cewa nan da ɗan lokaci zai ginawa Kanawa rijiya gaba dubu wacce ko da an shekara saran  ruwa toh sai tamfatse.

A laaaafiya baƙon Shehu Maghili !!!

Magaji Galadima
Kachallan Kano
Disamba 25, 2022.

 

Continue Reading

Hausa

Kano ba ta dace da APC ba – Bello Sharada

Published

on

APC Flag

Bello Muhammad Sharada

 

 

 

A tarihi Kano gari ne na ilimi. Kano gari ne na addini. Kano gari ne na kasuwanci. Kano gari ne na sarauta. Kano gari ne ‘yanci da walwala da tarbiyya. Kano ana yi mata kirari da Tumbin Giwa, jallabar Hausa ko da me ka zo an fika. Limisliki alfun.

Ka auna tarihin Sarakunan Kano na Hausa da Sarakunan Kano na Fulani. Ka koma yadda Kano take bayan Turawan mulkin mallaka sun zo har suka ci mu da yaki a 1903 da lokacin da aka bamu ‘yancin kai a 1960, da sanda aka kirkiro jihar Kano a 1967, da zamanin soja na Audu Bako da Sani Bello da Ishaya Aboi Shekari kafin a baiwa farar hula mulki a jamhuriya ta biyu a shekarar 1979 da zamanin mulkin Rimi da Abdu Dawakin Tofa da Sabo Bakin Zuwo a tsakanin shekara biyar 1979-1984. Da yanayin da gwamnonin  sojoji suka yi mulki a shekara 15 tun daga watan Augusta 1985 har zuwa watan Mayu 1999, aka yi gwamna Hamza Abdullah da Idris Garba da Ahmad Daku da Ndatsu Ummaru da Kabiru Gaya da Abdullahi Wase da Dominic Oneya da Aminu Isa Kwantagora basu saba da tsarin Kano ba sai a shekara bakwai da take hannun Hadimu.

Abin da ya jawo haka, an kauce tsarin Kaka da kakanni na siyasar Kano da tsarinta da dabi’unta. Jihar Kano ta dada sukurkucewa ne a zamanin mulkin APC na Gandujiyya. Duk girman Kano da daukakarta da yawan jama’a da Allah ya hore mata, mutum biyar ne kadai sai abin da suka shata, suka kitsa ko kana so ko baka so. Sun ce lokacinsu ne. Da sannu zasu tafi. Na farko gwamna Ganduje. Na biyu uwargidansa Farfesa Hafsat. Na uku Murtala Sule Garo. Na hudu Abdullahi Abbas. Na biyar Alasan Ado Doguwa. Mataimakin gwamna Ganduje sunansa ma Mota ba Fasinja saboda ba shi da wani tasiri, an ajiye shi safayar taya. Takarar gwamna da aka ba shi dole ce uwar naki. Shi kuma Usman Alhaji Sakataren gwamnati hoto ne. A gefe guda kuma suka dan dosana shugaban majalisar jiha Rt Hon Chidari. Wanda duk bai gamsu ba ya tambayi Dr Baba Impossible.

Babu wani abu da za a yi sai da izinin wadannan mutanen. Rigimar G7 da kafuwar NNPP ita ce kadai ta rage kaifin Goggo da Dan Sarki da Alasan Doguwa. Burin dan Sarki ya zama Sarki, burin Goggo kwamanda ya zama gwamna, burin Ganduje ya zama Sanata ko mataimakin shugaban kasa. Burin Alasan Ado Doguwa ya maye gurbin Femi Gbajabimilla.

SU biyar din nan  kowa da bukatar da ta hada su. Zaka gansu jumlatan, amma zuciyoyinsu daban-dabam. Dukkansu suna jifan juna. Murtala ya taba keta Alasan, ya taba cakume Abdullahi Abbas, a kwanan nan kuma Alasan Ado sai da ya mari Murtala a gaban Gawuna kuma a cikin gidansa. Alasan zai iya zagin kowa da sunan siyasa. Hatta Ahmed Aruwa sai da Alasan ya hankade shi a gaban mahaifiyarsa. A gaban Abdullahi Adamu shugaban jam’iyya na kasa na APC da gwamna Ganduje ya hayayyako wa Sardaunan Kano, har suka yi cacar baki da Aliko Dan Shuaiba, aka shiga tsakani. Yan wannan guruf din sune suka tsangwami Barau, an kai matsayin da Sanata Barau bai isa ya zo taro ba a Kano sai dai ya yi harkarsa a Abuja. Kwanan nan Sanata Barau ya baiwa Ganduje kyautar miliyan 150.

Abin da ya nace APC ba ta dace da Kano ba, a wadannan shekarun ne gwamna Ganduje ya kalli manyan masu daraja ya keta musu alfarma, sannan ya kirasu da Dattawan Wukari. A wannan lokacin ne gwamna ya dauki aikin da aka zabe shi domin ya aiwatar amma ya danka shi a hannun uwargidansa, har kuma ta nada wanda zai gaje shi.

An kai matsayin da komai ba a yinsa daidai a Kano a mulkin Ganduje. In kuma ka tanka sai a daureka. Ko a saka wasu karnuka su yi tayi maka haushi. GA Kano garin kasuwanci an yanka kasuwa ko ina ba tsari. Kullum a cikin rigimar fili. Kano garin Sarauta, ita kanta masarautar an yi mata filla-filla, Alasan Ado Doguwa ma Sardaunan kasar Rano ne, da rawaninsa ma ya kwankwashi bakin Murtala. Kano garin malanta, Council of Ulama sai da aka yi mata kishiya, hatta halifancin Tijjaniya sai da aka kutsa ga na Sarki ga na gwamna. Siyasa kuma ba a zancenta, Rarara ya taba zambo da tsulan biri aka yi masa tafi. Ya yi habaici da duna aka yi masa dariya. Ya buga misali da hankaka ana shirin kulle shi.

Babu wani lamarin APC da ake yi cikin adalci. Kowa kuka yake yi. Ga shi kansa Mai gidan APC na kasa babu wani abin alheri mai girma da aka yi wa jama’ar Kano a saboda kauna da biyayya da goyon baya da suke yi masa tsawon shekara 18.

APC bata dace Kano ba. A 2023 Sai an canza da kuri’armu cikin yardar Allah.

Bello Muhammad Sharada jigo ne a Siyasar gidan Malam Ibrahim Shekarau 

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending