Connect with us

Hausa

Marigayi Alhaji Bashir Usman Tofa: Mutum Mai Kyawawan Halaye Da Dabi’u Nagari

Published

on

Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun! Lallai daga Allah muke, kuma zuwa gare shi makomar mu take!!

Allahu Akbar! Yau litinin, 03/01/2022, mun wayi gari da wani mummunan labari mai sosa rai. Labari mai cike da bakin ciki marar iyaka. Labarin da ya girgiza arewacin Najeriya, da Najeriya baki daya. Labarin da yasa miliyoyan ‘yan Najeriya zubar da hawaye, domin tausayi da jimami, wato labarin rasuwar daya daga cikin dattawan arewa, masu kishin addini, masu kishi da tausayin talaka, masu kishin kasar su Najeriya da son ci gaban ta, kuma masu kishin yankin arewa; sauran ‘yan mazan jiya, baya-goya-marayu, wato Alhaji Bashir Usman Tofa.

Bashir Tofa ya rasu da asubahin yau litinin, bayan jinya da yayi na wasu kwanaki, kuma anyi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, a gidan sa dake Gandun Albasa, a cikin Birnin Kano. Jana’izar da dimbin al’ummah suka halarta.

Ina addu’a da rokon Allah ya jikan sa, ya gafarta zunuban sa, da kura-kuren sa, da kasawar sa. Allah yayi masa sakamako da Aljannah Firdausi. Allah ya albarkaci zuri’ar da ya bari, kuma Allah ya ba iyalan sa, ‘yan uwa, abokan arziki da al’ummar Musulmi baki daya, hakurin jure wannan babban rashi, amin.

Ya ku jama’ah! Lallai kyawawan dabi’u da halaye nagari na daga cikin muhimman abubuwan da addinin Musulunci ya ba fifiko, wanda ta hanyar mallakar su ne dan Adam zai iya samun tsira tun a nan duniya da kuma gobe kiyama. Kyawawan dabi’u da halaye nagari babbar alama ce da ke nuna nagartar mutum da kuma mutuncinsa. Ana gane mutumin kirki ta hanyarsu, kuma mafiya alherin Musulmi su ne wadanda suke da kyawawan halaye da dabi’u na gari. Kuma muminai masu cikakken imani wadanda Allah da ManzonSa suka fi so, kuma al’ummah suke kauna, sune masu kyawawan halaye da dabi’u na kwarai. Sannan kuma Musulmin kwarai shine wanda ya samu kyakkyawar tarbiyyah daga iyayensa, kuma ya mallaki wasu irin nagartattun dabi’u da halaye nagari abin koyi.

Allah Madaukaki ya yabi kyakkyawan hali da dabi’un Annabi (SAW) kuma Ya sanya shi ya zamo abin koyi ga dukkan Musulmi. Allah Madaukaki Yace:

“Kuma lallai, hakika kana a kan halayen kirki manya.” (Al-kur’an, 68:4)

Kuma lallai babbar manufar aiko Annabi (SAW) ita ce, ya dasa kyawawan halaye da dabi’u nagari tsakanin Musulmi, a cikin kowane fanni na rayuwarsu. Abu Hurairah (RA) ya ruwaito cewa:

“Manzon Allah (SAW) yace: “Hakika an aiko ni ne, domin in cika kyawawan halaye.” (Musnad na Imamu Ahmad)

A wata ruwayar Annabi (SAW) yace:

“Iyaka an aiko ni ne domin in cika kyawawan halaye.” (Muwadda Imamu Malik)

A wata ruwayar Annabi (SAW) yace:

“Hakika Allah Ya aiko ni ne domin in cika kyawawan dabi’u kuma in cika ayyuka na kwarai.” (Mujma’a al-Awsat)

’Yan uwa masu daraja! Kyakkyawar dabi’a a wurin Allah na nufin kayi riko da akida mai kyau da yin ayyukan Ibadah kamar yadda Manzon sa (SAW) ya koyar. A wurin mutane kuma, kyakkyawar dabi’a ko hali nagari, yana nufin ka zamo mai adalci, ka zamo mai tausayi, mai yafiya mai kirki, mai kyauta kuma mai hakuri a wurin mu’amala da su.

Kasancewar kyakkyawar dabi’a ko kyawon hali yana da matukar muhimmanci, sai riko da hali nagari ya zama wajibi a cikin addinin Musulunci. Manzon tsira, Annabi Muhammad (SAW) ya umarci Musulmi da su rika nuna halaye na gari a cikin kowane al’amari. Abu Zarril Ghifari (RA) ya ruwaito cewa:

“Annabi (SAW) yace: “Ka yi mu’amala da mutane da kyakkyawar mu’amala.” (Sunanut-Tirmizi)

Imam Ibn Al-kayyim yace:

“Addini gaba dayansa kyawawan halaye ne, don haka duk wanda yafi ka kyawon hali toh yafi ka a cikin addini.” (Madarij as-Salikin)

Kuma ya sake cewa:

“Kyakkyawan hali shine addini gaba daya.” (Madarij as-Salikin)

Abdullahi Ibn Amir ya ruwaito cewa, Manzon Allah (SAW) yace:

“Mafi alherinku shine mafi kyawun halinku.” (Buhari)

A wata ruwayar Annabi (SAW) yace:

“Mafiya cikar imani a cikin Musulmi, sune wadanda suka fi kyawon hali, kuma mafiya alherin cikinku sune wadanda suka fi kyautata wa matansu.” (Sunanut-Tirmizi).

Kuma a wata ruwayar Annabi (SAW) yace:

“Hakika, cikakkun muminai sune mafiya kyawun hali da kuma wadanda suka fi kyautata wa iyalansu.” (Sunanut-Tirmizi)

Abdullahi Ibn Amru yace:

“Manzon Allah (SAW) yace: “Shin in gaya maku mutumin da nafi so kuma yafi kusa da ni a ranar kiyama? Sune wadanda suke da kyakkyawan hali.” (Musnad Imamu Ahmad)

A wata ruwayar Annabi (SAW) yace:

“Hakika mafi soyuwa da kusanci da ni a taron Al-kiyama sune wadanda suka fi ku kyakkyawan hali. Kuma hakika mafiya zama abin kyama a wuri na daga cikin ku kuma mafiya nesa da ni a taron ranar Al-kiyama sune masu alfahari, masu almubazzaranci, masu girman kai.” (Sunanut-Tirmizi).

Domin yin koyi da yin biyayya da nuna da’a ga Allah da Manzon sa (SAW), da kuma girmama wadannan nassoshi, da girmama addinin Allah, yasa Alhaji Bashir Usman Tofa ya zamanto mutum mai kyawawan halaye da dabi’u masu kyau, kuma nagari.

A cikin shekaru ashirin da biyar da Allah ya hada ni dashi, tun daga 1997 zuwa yau da Allah ya karbi rayuwarsa, wallahi Allah shine shaida, ni ban san wannan bawan Allah da wasu munanan halaye ko dabi’u abin Allah waddai ba.

Allah yayi shi mai kyawawan halaye, da dabi’u masu kyau, wadanda duk wanda yayi mu’amala da shi, tabbas sai ya yabe shi.

Alhaji Bashir Usman Tofa zai baka shawara tsakanin sa da Allah, shawarar da wallahi ko dan cikinsa da ya haifa, iyakar shawarar da zai bashi kenan. Ba zai munafunceka ba, ba zai yaudare ka ba.

Idan aka kwana biyu bai ji ni ba, wallahi zai dauki waya ya kira ni, domin yaji ko lafiya. Kuma ban taba kiran sa yaki daukar kira na ba, duk da matsayin sa da girman sa, sai fa idan lokacin da na kira baya kusa da wayar, kuma idan ya ga kiran zai biyo ni da kira.

Duk lokacin da na shiga Kano, zan yi masa waya cewa na shigo, don haka zan zo in gaishe shi. Nan take zai sanar da masu gadi cewa, wane mai suna kaza zai zo, don haka ku bar shi ya shigo.

Duk Sallah karama da Sallah babba, sai yayi man sakon barka da Sallah.

Duk da wannan, a iya sani na da shi, Alhaji Bashir Usman Tofa mutum ne mai hakuri da yafiya. Mutum ne mai Ikhlasi (wato yin abu domin Allah). Shi mai kyakkyawar mu’amala ne ga ko wane mutum. Mutum ne mai son gyara a koda yaushe, mutum ne mai tsananin kishin addinin sa, mai kishin kasar sa mai kishin yankin sa na arewa.

Mutum ne shi mai kaunar Malaman addini, kuma mai yawan mu’amala ta mutunci da su.

Mutum ne mai yawan umurni da a aikata kyakkyawan aiki da kuma kokarin hani akan aikata mummunan aiki.

Alhaji Bashir Usman Tofa mutum ne mai yawan kiyaye harshensa daga surutu da maganganun banza, musamman marasa amfani. Amma fa idan a wurin fadar gaskiya ne, to baya shakkar ko wane mutum ko yaji tsoron sa. Ya kasance mutum mai yawan ibada, mai tausayi da saukin kai.

Bashir Tofa mutum ne mai tsantseni. Mutum ne marar rowa, wanda baya hana abun da aka roke shi, ko aka tambayeshi, sai fa idan baya da shi ne.

An shaide shi da cewa shi mutum ne mai karfin imani da tawakkali. Mutum ne mai tausayin marayu da son yara kanana. Mutum ne mai yawan yin rangwame da afuwa ga mutane, mai tsoron Allah da kamewa.

Alhaji Bashir Tofa mutum ne mai ciyar da abinci ga mabukata, mai son taimakon marasa karfi. Mutum ne mai fadin gaskiya komai dacinta, kuma baya shakkar duk abinda zai same shi wurin fadin gaskiyar. Yana da himma da kokari wurin girmama iyakokin Allah da dokokin sa. Shi mai sakin fuska ne ga mutane, miyagun mutane ne kadai baya saurara masu, kuma baya son zalunci da azzalumai. Haka nan baya kaunar rashin gaskiya, baya kaunar miyagun ‘yan siyasa da ashararai cikin al’ummah.

Ya kasance mutum mai rikon amana da cika alkawari; sannan gashi jarumi, mai karfin jarumtaka da rashin tsoro. Mutum ne karimi mai yawan karamci da hakuri tare da jurewa akan haka. Kuma gashi mutum yawan kunya.

Ya kasance mai kankan da kai, mai tawadu’u, mai yawan nuna rahama, tausayi da jin kai ga talakawa da kuma marasa galihu, kuma ga shi mai saukin kai, mai yafiya da hakuri kuma adali, mai tsananin tsoron Allah, kuma mai wadatar zuci da hakuri da kadan.

Ya kasance mai son yin alheri ga kowa da kowa; Musulmi da wanda ba Musulmi ba, kai hatta ma makiyansa alhairan sa sun kai gare su.

Bashir Tofa mutum ne mai son zaman lafiya, mai adawa da tsahin hankali ko rikici, ko zubar da jinin bayin Allah.

Bai nesanta kansa daga talakawa ba, yana tare dasu a koda yaushe, yana cudanya da su, kuma yana sauraron koke-koken su.

Shi mai kokari ne wurin zuwa gaishe da marasa lafiya, kuma ya biya kudin maganinsu (Hospital Bills), yayi masu alheri mai tarin yawa, Musulmi ne su ko kuma wadanda ba Musulmi ba. Sannan ga rashin girman kai, da yin godiya ga duk wanda yayi masa alheri, da kuma kokarin saka masa shi ma, da abunda zai iya.

Bashir Tofa mutum ne mai tsananin son dukkanin wani abu mai kyau da tsabta da kuma kamshi. Baya son datti, da kazanta da wari ko doyi.

Mutum ne mai son ganin al’ummah sun hada kai, baya son rarrabuwa da fada tsakanin al’ummah. Yana yawan shiga tsakani da kuma kokarin yin sulhu da sasanci tsakanin mutane.

Alhaji Bashir Usman Tofa yayi wa ilimi hidima matuka. Zaka fahimci wannan ta hanyar karanta rubuce-rubucen sa. Ya rubuta littafai masu dimbin yawa. Duk littafan da ya rubuta babu wanda bai bani ba da hannun sa. Kuma ya bani masu tarin yawa yace a raba wa bayin Allah masu son karatu.

A duk lokacin da ka samu damar yin fira da shi, wallahi zaka ji cewa damuwar sa har kullun ita ce, yaya za’a yi al’amarin kasar nan ya gyaru? Yaya za’a yi a samar da shugabanni nagari? Yaya za’a yi a samu zaman lafiya a arewa da Najeriya baki daya? Yaya za’a yi rayuwar talaka ta inganta? Yaya za’a yi al’ummah su hada kai domin a zauna lafiya? Kai ma a sani na, wallahi ya taba yin amfani da kudin aljihun sa, da dukiyar sa, yayi yawo, ya zagaya kasar nan, ya gana da Malamai daban-daban, wurin kokarin ganin ya hada kan Malaman addini.

Sannan ni dai a iya sani na, shine kadai mai kudi, kuma babban mutum, da ya samar da tsarin yin taruruka, tun daga matakin anguwanni. Kuma ko wane taro za’a yi da shi ake yi, tare da talakawa, wani lokaci ma a gidan sa ake yin taron. Duk wannan yana yi ne domin kokarin ciyar da al’ummah gaba.

Wadannan su ne kadan daga halaye da dabi’un Alhaji Bashir Tofa, wadanda Allah ya fahimtar da ni, a cikin ahekaru ashirin da biyar da nayi ina hulda da shi; dabi’un da wallahi duk wanda yayi hulda da shi, ko yake hulda da shi, zai shaida hakan.

Fata na, da roko na, shine, Allah yasa kyawawan aikin sa nagari su bishi. Allah ya haskaka makwancin sa, ya yalwata kabarin sa, amin.

Lallai kam al’ummah tayi babban rashi. An samu wani irin wawakeken gibi, wanda Allah ne kadai yasan yadda za’a cike shi.

Wassalamu Alaikum

Dan uwan ku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, Babban Limamin Masallacin Juma’ah na Nagazi-Uvete, da Masallacin Alhaji Abdurrahman Okene, da ke Okene Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa ta wannan lambar waya kamar haka: 08038289761.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Trending