Hausa
A kwanaki 100, VON ta farfaɗo, ci gaba ya bayyana da kuma fatan fin haka nan gaba – Ndace

Jibrin Baba Ndace
A zafin ranar 29 ga watan Oktoba, 2023 ne aka samu wani canji na alheri da ya lulluɓe harabar Voice of Nigeria (VON) mai cike da sa’ida, sakamakon naɗin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi mini a matsayin Darakta-Janar na gidan rediyon na ƙasa, inda hakan ya zamto wani ɗamba na sauyin zamani a kafar yaɗa labaran ta ƙasa.
Bikin karɓar aiki daga hannun wanda na gada, Osita Okechukwu ya wuce a ce biki ne na sallamar ma’aikaci. Da ga karɓar shugabancin, guguwar sauyi ta fara kaɗa wa bayan na halarci taron AFRICAST 2023 a Legas. Sai na yi amfani da wannan damar na ziyarci cibiyoyin watsa shirye-shiryen tashar ta mu da ke Ikoyi da Ikorodu, inda hakan ya bani kwarin gwiwar cewa akwai dama mai ƙarfi da zan samu na kawo gagarumin ci gaba a gidan rediyon.
Dawowa ta shelkwatar VON da ke Abuja kuma, sai na fuskanci akwai aiki ja a gaba na. A yanayin lalacewar gine-gine da kayan aiki da na gani a cibiyar mu ta Ikko, sai na ji cewa ya zama wajibi na tashi tsaye na kawo gyara cikin gaggawa.

Duk da cewa kusan hakan yanayin ya ke a cibiyar watsa shirye-shiryen mu ta Lugbe a Abuja, akwai abinda ya bani ƙarfin gwiwa, shi ne wutar sola da na tarar. Sai na fahimci cewa wato akwai ɗumbin nasarori a VON, amma ana buƙatar jajirtaccen shugaba da zai farfaɗo da ita.
Bayan gine-gine da kayan aiki, ma’aikata su ne ƙashin bayan VON, sai dai kuma kash! akwai ƙarancin karsashi a tare da su ma’aikatan gidan rediyon a duka tashoshin namu na Abuja da Legas sakamakon rashin biyan su alawus-alawus na su da kuma kuɗaɗensu na ƙarin matsayi. Wannan ƙalubale ne da ya ke buƙatar kawo ɗauki cikin gaggawa domin samun gaba mai kyau.
Tun asali, kamata ya yi a samu wani kundi na tsare-tsare. Zaburar da ma’aikata na buƙatar ƙirƙiro da dabarun inganta walwalar su da kuma ƙara musu matsayi akai-akai lokacin da ya dace da kuma basu lambobin yabo bisa ƙwazon su a aiki. Kada kuma a manta da cewa haɗin kai tsakanin shugabanni da ma’aikata shi ne babban sinadarin kawo sauyi Na ci gaba a ma’aikata.
Halastar mu zuwa babban taron UNESCO na duniya, karo na 42 da aka yi a birnin Paris da kuma taron ranar rediyo na duniya a Dubai, ba wai mun je yawon buɗe-ido ba ne, sai dai wata babbar dama ce ta samun damammaki daga ƙasashen duniya. Waɗannan tarukan wata babbar dama ce ta nuna wa duniya irin ƙwazon VON na watsa shirye-shirye daidai da yadda ya ke a duniya da kuma ƙulla alaƙa, duk a ƙoƙarin ta na zama a aji ɗaya da manyan kafafen yaɗa labarai na duniya.
Ganawar farko ta shugabannin VON da ta gudana a ranar 19 ga watan Disamba, 2023, ba wai an yi zaman hira ne kawai ba, sai dai zaman ya kasance wata ɗamba ce aka kafa wajen samar da haɗin gwiwa domin fitar da dabarun aiki da za su ƙara taimaka wa gidan rediyon ya cimma muradun sa.
Aiyuka na bi-da-bi me ya haifar da nasarar da mu ka samu ta ganawa da kwamitin majalisar dattawa kan yaɗa labarai da wayar da kan al’umma, kare kasafin kudin da mu ka yi wa kwamitocin majalisar dattawa da na majalisar wakilai da kuma ziyarar aiki da mu ka kaiwa Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da kan Al’umma, Alhaji Mohammed Idris. Waɗannan aiyukan sun kasance tubalin mu na gina alaƙa, wacce za ta samar mana da taimako da kuma fahimtar juna.
Hakazalika, alaƙar da mu ka ƙulla da ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu, da suka hada da Thunderbird, Image Marchants Promotions Limited, SEMEDAN, GOTNI, NIPR, Ciyaman na NUJ a Minna da kuma wakilci da ga Dangote Group da Jaiz Bank, ba wai ziyara ba ce kaɗai, sai dai sun zamto tattaunawa da za su buɗe kofa, su gina mana gadoji da kuma alaƙa da za su taimaka wa VON ta kai gaci.
Sannan, ziyarorin da muka kai wa Media Trust, National Orientation Agency, News Agency of Nigeria, Nigerian Diaspora Commission da NTA da kuma manyan shugabannin sojoji ya nuna ƙwazon mu na kawo gyara mai inganci a VON tare da bata suffar da ta ke buƙata.
A kwanaki 100 na farko a matsayin Darakta-Janar, na bada umarnin cewa duk wani ɗan hidimar ƙasa (NYSC) da masu koyon aiki a VON, dole a basu horo na musamman, da nufin su ji a ransu kamar su ma ma’aikata ne a tsawon lokacin da za su yi a gidan rediyon. Daɗin daɗawa kuma mun ƙulla alaƙa da Guards Polo Club da ƙungiyar shugabannin ma’aikatu ta Afirka domin jawo hankalin al’umma ga irin aikace-aikacen VON.
Bayan duk wadannan, irin bayanan sam-barka da ke fitowa daga bakunan ma’aikatan VON masu albarka, ya ƙara mana ƙaimi da ƙwarin gwiwa. Maida hankali da mu ka yi wajen gyara lalatattun kayan aikin mu da neman tallafin gwamnati wajen farfaɗo da tashar mu ta Lugbe ya nuna yadda shugabancin mu ke da zuciyar kawo gyara da kuma ɗaukaka VON.
A yayin da muka cika kwanaki 100 da karɓar ragamar shugabancin VON, magana a ke yi ta fara ganin guguwar sauyi ta fara kaɗa wa. Kalubalen da mu ka taras ya zamto wani ginshiƙi na gyara mai inganci. Sannan, dabarun da mu ke ɓullo da su sau ɗau saiti na fito dartabar VON ba wai a matsayin shahararren gidan rediyo ba, har ma ta zamto a bar koyi a fannin watsa shirye-shirye a faɗin duniya. Yayin da ake ci gaba da samar da hanyoyin gyara, lokaci kaɗai mu ke jira da zai fito da VON da har karan ta zai kai tsaiko a idon duniya.
Mallam Jibrin Ndace shi ne Darakta-Janar na VOICE of Nigeria, VON. Tashar watsa labarai na duk duniya ta Nijeriya.

Hausa
FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.
KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.
Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.
“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”
“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”
SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.
While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.
In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.
There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.
NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.
NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.
