Connect with us

KANUN LABARAI

Ganduje zai sanya ranar Mukabala da Abduljabbar Kabara

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

A yau Litinin ne ake sa ran za a mikawa gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje rahoton kwamitin da aka kafa da zai shirya mukabala tsakanin Malam Abduljabbar Kabara da sauran Malam jihar Kano.

Kano Focus ta ruwaito kwamishinan al’amuran addinai na jihar Kano dakta Tahar Adamu Baba Impossible ya sanar da hakan a yau Litinin.

Baba Impossible ya ce mutane basu fahinci sakon da aka fitar tun da fari ba, inda ya ce dama can gwamnati bata ce za a gudanar da mukabalar cikin makonni biyu masu zuwa ba.

Ya ce gwamnan Kano ya baiwa kwamitin da aka kafa ne mako biyu ya mika rahotonsa.

A cewarsa yanzu kuma kwamitin ya kammala aikinsa a yau Litinin, kuma zai mika rahoton ga gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje.

Haka zalika ana sa ran da zarar Gandujen ya nazarci rahoton zai sanya ranar da za a zauna domin gudanar da mukabalar.

“Ai ba cewa aka yi a mako biyu za a yi mukabala ba, cewa akayi gwamnati ta ce a je a shirya cikin mako biyu a zomata da rahoto.

“Duk kwamitin da aka kafa sun kammala rahotonsu za kuma a mikawa mai girma gwamnan ranar Litinin.

“Bayan gwamna yayi studying din rahoto ya kammala zai sa ranar da za a yi.

“Amma su malamin a bangarensu shirinsu za su yi, ba shirin gwamnati ba ne.

“Amma shirin gwamnati kwamitoci sun zazzauna da wadanda za a gayyato daga wajen Kano an fadesu, da wadanda za a gayyato na ciki gida an gayyacesu, da jami’a tsaro da waye duk an gama an kammala.

“Yanzu sai mu saurari abinda gwamnati za ta ce, ita take da ikon sa rana, dama bata ce yau za a yi mukabalaba, ta ce ta bada mako biyu a shirya.

Game da kiraye-kirayen da wasu malamai ke yi na cewa bai kamaya a yi mukabalarba.

Babba Impossible ya ce ko kadan ba za su saurari korafin malaman ba, za su ci gaba da shirinsu na ganin anyi mukabalar.

Haka zalika ya ce malamai sun kawo karafin Abduljabbar, shi kuma ya nemi ayi masa adalci, don haka gwamnati za ta baiwa kowanne bangare hakkinsa.

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending