Hausa
Shekara 60 na Hausawa a Doron Ƙasa (1) – Farfesa Malumfashi

Farfesa Malumfashi
Wannan wani raddi ne da Farfesa Ibrahim Malumfashi ya yi wa Abduljalil Ismail Ajis
Afwan, na so na dawo da zancen a sahar da ka yi naka martanin, amma da na leƙa sai na ga ba mutane da yawa a wurin da za a iya tattaunawa, a ƙaru, shi ya sa na dawo da mu a nan. Ko ba komi nan ne asalin batun tun farko.
Abubuwa uku ke da muhimmanci daga martanin da ka yi kan nawa batun, kuma su ne za su yi mana jagora daga yau, ISA.

1. Asalin samuwar Ɗan Adam da samuwar al’ummar Hausawa da sauran al’ummar duniya da harsunansu da al’adu.
2. Abu na biyu shi ne mu tambayi kanmu ko al’ummar Hausawa sun rayu a wasu yankuna na duniya kafin su zaune a yankin ƙasar Hausa da suke yanzu ko kuwa dai ba wata al’ummar da za a kira da Hausawa sai Maguzawa da muka saba ji da gani, waɗanda za a kira da kifin rijiya?
3. Shin babu wasu kalmomi ko jumloli ko batutuwa na asali da Hausawa suka gada daga samuwar ɗan Adam tun daga aljanna har zuwa doron ƙasa da bayan ruwan ɗufana da samuwar ɗan Adam na zamani daga shekara ta dubu 150. Idan Hausawa sun rayu a waɗannan zanguna, wanda ba a iya ƙaryatawa kai tsaye; (a kula, ina magana ne kan Hausawa, wato al’umma a nan, ba masu harshe ko magana da Hausa a yau ba,) to kuwa waɗannan mutane sun taho da rayuwar waɗancan zamunna, kuma sun ci gaba da tu’ammali da su zuwa wani lokaci suka ɓata daga baya suka sake cin karo da su a zamantakewa ta zamani.
A saha irin haka da muke irin wannan tattaunawa, inda ba cikakken aji ba ne da za a iya darje komi ya fito fili, dole a samu irin wannan tunani naka da ma wasu irin ka, kamar yadda aka samu a ‘yan kwanakin nan dangane da asalin Hausawa.
Ba na yi wancan rubutu ba ne domin koɗa ko nuna isa ta Hausawa da neman ɗora su a matsayin da ba nasu ba, na yi ne saboda haka batun yake, abin da aka karantar da ni da kuma abubuwan da na yi nazari ne a tsawon shekaru, wannan ya nusar da ni cewa Hausawa mutane da suka rayu kamar sauran al’ummar duniya, ba su da bambanci da sauran al’umma ta fannin asalin bil Adama, sai dai wani abu da yawancin mutane masu nazari da sharhi ba su kai hannu gare shi ba shi ne, bincike na asalin Hausawa ya wuce abin da aka saba ji, wato daga shekara dubu 1 ko 2 ko 3 ko kuma 5 da ake tsayawa.
Wannan ne ya sa kai da masu irin naka tunanin ke ganin ina ma aka san wasu Hausawa a doron ƙasa, domin Hausawa ba kowan kowa ba ne da za a haɗa su da Larabawa ko Girkawa ko Yahudawa ko Asiyawa da makamantan su, sai ka ce su waɗannan da ake magana kai, tun daga farkon rayuwa su kaɗai aka halitta!
Saboda daidaita tunani zan ƙoƙarta tattaɓo wasu daga cikin waɗannan matsaloli da ake fuskanta ISA. Na so na yi bayanin irin na malamin jami’a da ke magana da masana ‘yan uwansa a fagen nazari, ana yi ana kawo tushen bayani domin kafa hujja, amma ba zai samu ba, saboda sahar fesbuk ba jami’a ba ce da ƙila kowa zai iya fahimtar inda aka fito da inda ake da yadda aka samu matsaya game da batutuwa irin wannan. Amma in na kammala tattaunawar ISA, ƙila cikin kwana 3 ko 4 nan gaba, zan ajiye maka manazarta da za ka bibiya domin tabbatar da abin da na faɗa ko ƙaryatawa ko kuma samun ƙarin haske.
Wannan fage na asali da samuwar ɗan Adam da kuma Hausawa, masana da dama sun taɓo waɗannan batutuwa masu rikitarwa a wurare da dama da ba lokacin da zan daddage su saboda kafa hujja, amma ga abubuwa uku da za su iya yi mana jagora kafin mu ci gaba da faɗaɗa tunanin.
Farfesa Ibrahim Malumfashi malami ne a Jami’ar jihar Kaduna ya wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.
KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.
Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.
“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”
“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”
SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.
While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.
In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.
There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.
NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.
NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.
