Connect with us

KANUN LABARAI

Babbar Kotu a Kano ta dakatar da karamar kotu tuhumar shugaban Hukumar KAROTA

Published

on

Aminu Abdullahi

Babbar kotun jihar Kano mai lamba bakwai ta dakatar da kotun majestiri mai lamba 12 daga ci gaba da sauraron shari’ar zargin  cin hanci da rashawa da ake yiwa shugaban Hukumar KAROTA Bappa Babba Dan Agundi.

Kano Focus ta ruwaito mai shari’a Malam Usman Na’abba ne ya bada umarnin  dakatarwar ranar Litinin har sai babbar kotun ta duba ko ma karamar kotun na da hurumi umartar wanda ake kara da ya bayyana da kansa a gabanta.

Haka kuma ta sanya ranar 26 ga watan Oktoba da muke ciki domin fara nazartar shari’ar da aka faro a karamar kotun.

Tun da fari dai lauyan da ke kare shugaban hukumar Karota Barista Mutawakil Ishaq Muhammad, ne ya garzaya babbar kotun yana kalubalantar hukuncin da kotun Majistiret mai lamba 12 karkashin mai shari’a Muhammad Jibril da ta nemi shugaban Hukumar ta KAROTA Bappa Babba Dan Agundi ya gurfana a gaban ta ba tare da wakilci ba.

Idan ba a manta ba dai wani direban Adai-daita sahu Abdullahi Yahya Mai Sango ne ya shigar da karar gaban kotun Majestiri yana kalubalantar Baffa Babba Dan Agundi bisa laifin cin hanci da rashawa da kuma cuta kan na’urar Tracker.

Hakan ta sanya kotun majistirin ta aike da sammaci har sau biyu ga Dan Agundi da ya bayyana a gaban ta sai dai hakan yaci tura.

Sai dai lauyan mai kara Barista Abba Hikima Fagge yace dakatarwar da babbar kotun tayi na ci gaba da sauraron shari’ar a karamar kotun ba yana nufin mista Dan Agundi ba zai bayyana a gaban kotu ba.

A cewar sa hakan zai kawo tsaiko ne kawai amma da zarar babbar kotun ta kamala nazarin ta za ta bada umarini ya bayyana.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending