KANUN LABARAI
Dalilan da ya sa marasa lafiya a Kano suka zabi zuwa ‘kyamis’ maimakon asibiti
Aminu Abdullahi
Dayawa daga cikin marasa lafiya a Kano musamman ma masu karamin karafi sun zabi su je kyamis domin duba lafiyarsu maimkon asibti.
Wani bincike da jaridar Kano Focus ta yi ta gano yadda kyamis ke cika da marasa lafiya da ke neman aduba lafiyar su kamar a asibiti.
Muhammad Tukur Ibrahim da ke Gwauron Dutse a nan Kano marar lafiya ne da aka iske akan layin jiran mai kyamis, ya ce ba zai iya zuwa asibiti domin a duba shi ba.
Ya ce akwai dogon layi a asibiti, da komai ma ka iya samun mutum kafin azo kansa ga babu kulawar da ta da ce.

“Idan na kamu da rashin lafiya kyamis nake garzayawa, nan ne da naje za a yi min allura abani yan kwayoyi na dawo gida.
“Indai na je asibiti to sai idan lamarin ya ta’azzara naji alamar kamar zan mutu” acewar sa.
“Ma’aikatan lafiya a asibiti basa kula marasa lafiya yadda ya kamata, ga kyara da tsangwama.
“Hakan ta sanya marasa lafiya da dama kauracewa zuwa asibiti domin ko sunje da bakin cikin ma’aikatan za su dawo” ya kara da cewa.
Ita kuwa wata marar lafiyar da itama aka iske a layin Kyamis Hajara Isma’il dake Unguwar Mariri ta talauci ne kawai ke sata zuwa kyamis.
Ta ce komai tsananin cuta gwara taje kyamis tun da ko taje asibitin ma bata da kudim ganin likita.
Ta kara da cewa mafiya yawan likotoci da malaman jinya a sibitoci basu da kirki basa ganin darajar mutum ko kadan.
“Idan kaje asibiti za kaga yadda suke dakawa marasa lafiya tsawa, su kuma wulakantasu yadda suka ga dama, hakan ta sanya gwara muje kyamis.” Ta ce.
Shi ma wani mazaunin Gwammaja a nan Kano Khalipha Yunusa ya ce ma’aikatan jinya a asibiti sun wulakantashi yadda ba a zato akan bin layin asibiti.
Ya ce yadda ma’aikatan lafiya ke yiwa marasa lafiya a sibiti abin kare ba zai ci ba.
A don hakan ne ma ya ce gwanda ya yi tafiyar sa kyamis ya bada yan kudi tsirari a duba shi.
Ko akwai matsala karbar magani a kyamis
Wani dan jarida a nan Kano Abdulkaren Muhammad da ke unguwar Tukuntawa ya ce kiris ya rage ya rasa idanunsa sakamakon maganin da aka bashi a kyamis.
Ya ce lokacin da ya fara jin ciwon ido sai ya tafi kyamis domin a duba shi aka kuma bashi wani magani da ya yi amfani da shi sama da mako guda.
Sai da a cewar sa da yake ba likita ne ya auna shi ya bashi maganin ba kadan ya rage ya rasa idon nasa baki daya.
“Da naje Kyamis na yi masa dukkanin bayanin abin da ke damuna sannan ya dauko magani ya bane ba tare da anyi gwaji ba da hakan y kusan makantar da ni” ya ce.
Nasir Mustapha Salanta, shi ma ya sahida irin hadarin da ya fada game da karbar magani a kyamis.
Ya ce ko kadan ba zai kara zuwa kyamis karbar magani ba domin kuwa hakan ya kusan salwantar da rayuwar sa.
A cewarsa komai dogon layi gwanda ya je asibiti likita ya dubashi ya bshi magani.
Dalilan da yasa muke bada magani a kyamis
Sai dai a tattaunawar jaridar Kano Focus da wasu masu kyamis a nan Kano kan dalilian da ya sanya suke duba marasa lafiya su kuma ba likitoci ba sun ce akwai dalili.
Wani mai kyamis a unguwar Tukuntawa Ahmad Umar ya ce mafiya yawan masu kyamis basa bin dokar da aka gindaya na sayar da magani.
Ya ce a ayanzu kyamis waje ne kawai na nenan kudi da al’umma kuma suke taimakawa a tara.
Ya ce akwai da dama masu kyamis da ke rubutawa marasa lafiya magani sakaka ba tare da sanin me ke damun sa.
“Ko da yake bana cikin irin wadannan masu kyamis din amma dai masu kyamis suna abin da suka ga dama.
“Duk wanda ya zo siyan magani wajen ba tare da takardar da likita ya rubuta ba nakance masa koma ka ga likita” a cewar sa.
Shi ma wani mai kyamis Zaidu Salisu Falalu ya ce da gaskene masu kyamis na baiwa marasa lafiya magani ba tare da sanin me ke damun suba.
Sai dai ya ce ba duka ba ne aka taru aka zama daya, domin shi dai yana iya kokarin sa.
Ya ce yakan tambayi marasa lafiya kon sun yi gwaji kafin ya ce zai basu magani.
Sai dai ya ce idan yaga lamarin kamar ya tsananta to sai ya basu magani ko kuma ya yi musu allura.
Ko litoci na sane da wannan al’amari?
Tsohon shugaban kungiyar likotoci ta kasa reshen jihar Kano Sunusi Muhammad Bala ya ce doka ta tanadarwa masu kyamis yadda za su gudanar da sana’ar su.
A cewar sa abin da akasan kyamis da shi shi ne ya bada taimakon gaggawa, ya kuma sayar da magani idan likita ya rubuta.
Dakta Bala ya ce ko kadan ba aikin mai kyamis ba ne ya yiwa marasa lafiya gwaji ko kuma ya basu maganin cuta.
Ya kuma ce dukkanin marar lafiyar da ya zabi ya dinga zuwa kyamis domin a duba lafiyarsa to kuwa lafiyar sa ba za ta taba dai-daita ba.
“Abin da masu kyamis za su ce ko kana da typhoid da malaria su kuma baka magnain da zai iya kashe ka.”
Dakta Bala ya ce kungiyarsu ta aike da wani kudirin doka gaban zauren majalisar jiha da zai dinga daukar mataki kan masu yi musu sojan gona a ayyukan su.
Ya kuma ce kudirin dokar idan aka amince da shi zai hukunta dukkanin ma’aikatan lafiyan da suke shiga ayyukan likitoci suna fakewa.
Ya kuma shawarci jama’a da akowanne lokaci su guji jefa lafiyar su cikin hadari.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
