KANUN LABARAI
Dalilan da ya sa marasa lafiya a Kano suka zabi zuwa ‘kyamis’ maimakon asibiti
Aminu Abdullahi
Dayawa daga cikin marasa lafiya a Kano musamman ma masu karamin karafi sun zabi su je kyamis domin duba lafiyarsu maimkon asibti.
Wani bincike da jaridar Kano Focus ta yi ta gano yadda kyamis ke cika da marasa lafiya da ke neman aduba lafiyar su kamar a asibiti.
Muhammad Tukur Ibrahim da ke Gwauron Dutse a nan Kano marar lafiya ne da aka iske akan layin jiran mai kyamis, ya ce ba zai iya zuwa asibiti domin a duba shi ba.
Ya ce akwai dogon layi a asibiti, da komai ma ka iya samun mutum kafin azo kansa ga babu kulawar da ta da ce.

“Idan na kamu da rashin lafiya kyamis nake garzayawa, nan ne da naje za a yi min allura abani yan kwayoyi na dawo gida.
“Indai na je asibiti to sai idan lamarin ya ta’azzara naji alamar kamar zan mutu” acewar sa.
“Ma’aikatan lafiya a asibiti basa kula marasa lafiya yadda ya kamata, ga kyara da tsangwama.
“Hakan ta sanya marasa lafiya da dama kauracewa zuwa asibiti domin ko sunje da bakin cikin ma’aikatan za su dawo” ya kara da cewa.
Ita kuwa wata marar lafiyar da itama aka iske a layin Kyamis Hajara Isma’il dake Unguwar Mariri ta talauci ne kawai ke sata zuwa kyamis.
Ta ce komai tsananin cuta gwara taje kyamis tun da ko taje asibitin ma bata da kudim ganin likita.
Ta kara da cewa mafiya yawan likotoci da malaman jinya a sibitoci basu da kirki basa ganin darajar mutum ko kadan.
“Idan kaje asibiti za kaga yadda suke dakawa marasa lafiya tsawa, su kuma wulakantasu yadda suka ga dama, hakan ta sanya gwara muje kyamis.” Ta ce.
Shi ma wani mazaunin Gwammaja a nan Kano Khalipha Yunusa ya ce ma’aikatan jinya a asibiti sun wulakantashi yadda ba a zato akan bin layin asibiti.
Ya ce yadda ma’aikatan lafiya ke yiwa marasa lafiya a sibiti abin kare ba zai ci ba.
A don hakan ne ma ya ce gwanda ya yi tafiyar sa kyamis ya bada yan kudi tsirari a duba shi.
Ko akwai matsala karbar magani a kyamis
Wani dan jarida a nan Kano Abdulkaren Muhammad da ke unguwar Tukuntawa ya ce kiris ya rage ya rasa idanunsa sakamakon maganin da aka bashi a kyamis.
Ya ce lokacin da ya fara jin ciwon ido sai ya tafi kyamis domin a duba shi aka kuma bashi wani magani da ya yi amfani da shi sama da mako guda.
Sai da a cewar sa da yake ba likita ne ya auna shi ya bashi maganin ba kadan ya rage ya rasa idon nasa baki daya.
“Da naje Kyamis na yi masa dukkanin bayanin abin da ke damuna sannan ya dauko magani ya bane ba tare da anyi gwaji ba da hakan y kusan makantar da ni” ya ce.
Nasir Mustapha Salanta, shi ma ya sahida irin hadarin da ya fada game da karbar magani a kyamis.
Ya ce ko kadan ba zai kara zuwa kyamis karbar magani ba domin kuwa hakan ya kusan salwantar da rayuwar sa.
A cewarsa komai dogon layi gwanda ya je asibiti likita ya dubashi ya bshi magani.
Dalilan da yasa muke bada magani a kyamis
Sai dai a tattaunawar jaridar Kano Focus da wasu masu kyamis a nan Kano kan dalilian da ya sanya suke duba marasa lafiya su kuma ba likitoci ba sun ce akwai dalili.
Wani mai kyamis a unguwar Tukuntawa Ahmad Umar ya ce mafiya yawan masu kyamis basa bin dokar da aka gindaya na sayar da magani.
Ya ce a ayanzu kyamis waje ne kawai na nenan kudi da al’umma kuma suke taimakawa a tara.
Ya ce akwai da dama masu kyamis da ke rubutawa marasa lafiya magani sakaka ba tare da sanin me ke damun sa.
“Ko da yake bana cikin irin wadannan masu kyamis din amma dai masu kyamis suna abin da suka ga dama.
“Duk wanda ya zo siyan magani wajen ba tare da takardar da likita ya rubuta ba nakance masa koma ka ga likita” a cewar sa.
Shi ma wani mai kyamis Zaidu Salisu Falalu ya ce da gaskene masu kyamis na baiwa marasa lafiya magani ba tare da sanin me ke damun suba.
Sai dai ya ce ba duka ba ne aka taru aka zama daya, domin shi dai yana iya kokarin sa.
Ya ce yakan tambayi marasa lafiya kon sun yi gwaji kafin ya ce zai basu magani.
Sai dai ya ce idan yaga lamarin kamar ya tsananta to sai ya basu magani ko kuma ya yi musu allura.
Ko litoci na sane da wannan al’amari?
Tsohon shugaban kungiyar likotoci ta kasa reshen jihar Kano Sunusi Muhammad Bala ya ce doka ta tanadarwa masu kyamis yadda za su gudanar da sana’ar su.
A cewar sa abin da akasan kyamis da shi shi ne ya bada taimakon gaggawa, ya kuma sayar da magani idan likita ya rubuta.
Dakta Bala ya ce ko kadan ba aikin mai kyamis ba ne ya yiwa marasa lafiya gwaji ko kuma ya basu maganin cuta.
Ya kuma ce dukkanin marar lafiyar da ya zabi ya dinga zuwa kyamis domin a duba lafiyarsa to kuwa lafiyar sa ba za ta taba dai-daita ba.
“Abin da masu kyamis za su ce ko kana da typhoid da malaria su kuma baka magnain da zai iya kashe ka.”
Dakta Bala ya ce kungiyarsu ta aike da wani kudirin doka gaban zauren majalisar jiha da zai dinga daukar mataki kan masu yi musu sojan gona a ayyukan su.
Ya kuma ce kudirin dokar idan aka amince da shi zai hukunta dukkanin ma’aikatan lafiyan da suke shiga ayyukan likitoci suna fakewa.
Ya kuma shawarci jama’a da akowanne lokaci su guji jefa lafiyar su cikin hadari.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
