Connect with us

KANUN LABARAI

Rufin asirin amarya: An fara bayar da hayar kayan kicin na amare a Kano

Published

on

 

Zulaiha Danjuma

Wani dan Kasuwa a nan Kano da ke kasuwar Sabon Gari Usman Mustaph, ya fara bayar da hayar kayan kicin ga amaren da za a yiwa aure kuma iyayen su ba su da halin saya.

A wata hira ta musamman da jaridar Kano Focus Usman ya ce sun fito da wannan sana’ar ne domin tallafawa sabbin amare da iyayensu kar su ji kunya.

Ya ce duk mai bukata za a bashi hayar kayan kicin na sati daya akan kudi N20,000, na sati biyu kuma N35,000 ya yin da suke bayar da na wata guda akan kudi N70,000.

Ya ce ‘yan mata masu yiwa samari gara, ana basu hayar filas na shayi, ko filas na zuba abinci don dai a birge saurayi idan yazo zance.

Sai dai ya ce akwai sharudda masu tsauri game da kayan nasu da sai mai karba ya amince sannan za a bashi.

Sharadin shi ne duk wanda ya fasa ko ya lalata wani abu daga cikin kayan da ya karba to zai biya kudin sabo.

Haka kuma idan aka kara kwana guda daga cikin kwanakin da ka kayyade to za a ci tarar mai karba wasu kudade na musamman.

Ko an fara karbar?

Malam Mustapha ya ce tun daga ranar da ya kaddamar da shirinsa na fara wannan sana’a jama’a da dama ke kiran sa a waya domin neman karba.

Ya ce a rana yakan karbi waya sama da goma duk na mabukata karbar hayar kayan.

A don hakan ne ma ya ce ba zai fara baiwa kowa ba sai ya gudanar da shiri na musamman da zai taimakawa kasuwancin nasa.

Ya kara da cewa ba wai jama’ar Kano ba harma daga jihohin Sokoto Zamfara Kaduna Da Jigawa ana kiransa domin karbar kayan.

“Abinda muke yi yanzu shi ne tallata hajar mu domin muga shin mutane ma za su karba ko akasin haka.

“Mutane na kirana suna ce min suna bukatar kayan, don Allah mu yi sauri mu fara kuma da zarar mun fara mu sanar da su.

Ko hakan zai haifar da ‘DA mai ido?

Wata malama da ke ba da shawarwari ga mata kan al’amuran aure dake kungiyar Idyllic Coaching and Counseling Services Khadija Ibrahim ta ce  wannan al’amari da ya kunno kai ba zai haifar da ‘da mai ido ba.

A cewarta mata da maza yanzu sun fada rayuwar karya na karbar hayar kayan lefe su kuma mata hayar kayan daki da hakan ke kashe aure saki ba kaidi.

Ta ce karbar irin wadannan kayayyaki na nufin mika kai ga rayuwar karya, rashin gasgata juna da hakan ke kassara aure.

Son a Burge

A cewar malama Khadija mafiya yawan wadan da ke fadawa cikin wannan al’amari na bukatar a ce sun burge ne kawai.

“Mutane na bukatar burge jama’a su nuna arziki bayan a zahiri karansu ba kai tsaiko ba.

“kuma duk wannan al’amarin ana son burge ‘yan soshiyal media ne kaiwai, kuma da zarar ka burge su ka jefa kanka cikin hadari.”

“Nasha jin labarin mazan da ke karbar hayar akwatun lefe bayan sati biyu da auren sai kaji ance barayi sun haura.

Sakamakon yin ‘dage

Malama Khadija ta ce mutane a wannan zamani na son yin rayuwar ‘dage’ da hakan  ke jefa su cikin rudani da rashin samun nasarar auren.

“A wannan zamanin jama’a na yi rayuwar karya wajen aurensu da kuma kowa ya san karya bata dorewa.

“Lokaci na nan zuwa da abokin zamanka ko abokiyar zamanka za ku fuskanci karya kuka shirya kan ku.

“Idan kuka fahinci cewar wadannan kayan kicin din, wadannan lefen da sauran su duk haya kuka karba to a nan ne fa za ku fara gane irin matsalar da kuka jefa kanku.” Ta ce

Hayar Lefe

Wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ta gano samari da yawa na karbar hayar akwatinan lefe da ma lefen kansa a wasu lokutan.

Ibrahim Idris wani dan kasuwa a nan Kano ya ce ya karbi hayar akwatunan lefe ne saboda yana son yin auren amma kudaden sa ba za su is aba.

“Na karbi hayar akwatunan lefen ne saboda kudin lefe na ba zai isa har na sayi akwatin ba.

“Kuma matata bata taba ganewaba saboda naje na biya kudin da kandan kadan har na kammala biya” a cewar sa.

Shi kuwa wani mai sana’ar tuka baburin adai-daita Sahu Garzali Shu’ibu ya ce ya karbi hayar akwatunan kayan lefe da kayan a ciki baki daya.

“Na karbi hayar akwatunan lefe makare da kaya sai dai abin takaici matata ta bankado ni.

“Masu kayan suka dinga zuwa gidana saboda na kasa biyan su ban iya biyan kayan ciki ba balantan akwatunan.

“Haka kawai wata rana suka zo gidan suka gayawa matata komai.

“Baya da na dawo ne ta fara tambayata ya akayi na hada lefen da na kai mata?

“Hakan ya sanya rigimar yau daban ta gobe daban daga karsehe dai ta bar gidan.” Ya ce.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending