Connect with us

KANUN LABARAI

Rufin asirin amarya: An fara bayar da hayar kayan kicin na amare a Kano

Published

on

 

Zulaiha Danjuma

Wani dan Kasuwa a nan Kano da ke kasuwar Sabon Gari Usman Mustaph, ya fara bayar da hayar kayan kicin ga amaren da za a yiwa aure kuma iyayen su ba su da halin saya.

A wata hira ta musamman da jaridar Kano Focus Usman ya ce sun fito da wannan sana’ar ne domin tallafawa sabbin amare da iyayensu kar su ji kunya.

Ya ce duk mai bukata za a bashi hayar kayan kicin na sati daya akan kudi N20,000, na sati biyu kuma N35,000 ya yin da suke bayar da na wata guda akan kudi N70,000.

Ya ce ‘yan mata masu yiwa samari gara, ana basu hayar filas na shayi, ko filas na zuba abinci don dai a birge saurayi idan yazo zance.

Sai dai ya ce akwai sharudda masu tsauri game da kayan nasu da sai mai karba ya amince sannan za a bashi.

Sharadin shi ne duk wanda ya fasa ko ya lalata wani abu daga cikin kayan da ya karba to zai biya kudin sabo.

Haka kuma idan aka kara kwana guda daga cikin kwanakin da ka kayyade to za a ci tarar mai karba wasu kudade na musamman.

Ko an fara karbar?

Malam Mustapha ya ce tun daga ranar da ya kaddamar da shirinsa na fara wannan sana’a jama’a da dama ke kiran sa a waya domin neman karba.

Ya ce a rana yakan karbi waya sama da goma duk na mabukata karbar hayar kayan.

A don hakan ne ma ya ce ba zai fara baiwa kowa ba sai ya gudanar da shiri na musamman da zai taimakawa kasuwancin nasa.

Ya kara da cewa ba wai jama’ar Kano ba harma daga jihohin Sokoto Zamfara Kaduna Da Jigawa ana kiransa domin karbar kayan.

“Abinda muke yi yanzu shi ne tallata hajar mu domin muga shin mutane ma za su karba ko akasin haka.

“Mutane na kirana suna ce min suna bukatar kayan, don Allah mu yi sauri mu fara kuma da zarar mun fara mu sanar da su.

Ko hakan zai haifar da ‘DA mai ido?

Wata malama da ke ba da shawarwari ga mata kan al’amuran aure dake kungiyar Idyllic Coaching and Counseling Services Khadija Ibrahim ta ce  wannan al’amari da ya kunno kai ba zai haifar da ‘da mai ido ba.

A cewarta mata da maza yanzu sun fada rayuwar karya na karbar hayar kayan lefe su kuma mata hayar kayan daki da hakan ke kashe aure saki ba kaidi.

Ta ce karbar irin wadannan kayayyaki na nufin mika kai ga rayuwar karya, rashin gasgata juna da hakan ke kassara aure.

Son a Burge

A cewar malama Khadija mafiya yawan wadan da ke fadawa cikin wannan al’amari na bukatar a ce sun burge ne kawai.

“Mutane na bukatar burge jama’a su nuna arziki bayan a zahiri karansu ba kai tsaiko ba.

“kuma duk wannan al’amarin ana son burge ‘yan soshiyal media ne kaiwai, kuma da zarar ka burge su ka jefa kanka cikin hadari.”

“Nasha jin labarin mazan da ke karbar hayar akwatun lefe bayan sati biyu da auren sai kaji ance barayi sun haura.

Sakamakon yin ‘dage

Malama Khadija ta ce mutane a wannan zamani na son yin rayuwar ‘dage’ da hakan  ke jefa su cikin rudani da rashin samun nasarar auren.

“A wannan zamanin jama’a na yi rayuwar karya wajen aurensu da kuma kowa ya san karya bata dorewa.

“Lokaci na nan zuwa da abokin zamanka ko abokiyar zamanka za ku fuskanci karya kuka shirya kan ku.

“Idan kuka fahinci cewar wadannan kayan kicin din, wadannan lefen da sauran su duk haya kuka karba to a nan ne fa za ku fara gane irin matsalar da kuka jefa kanku.” Ta ce

Hayar Lefe

Wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ta gano samari da yawa na karbar hayar akwatinan lefe da ma lefen kansa a wasu lokutan.

Ibrahim Idris wani dan kasuwa a nan Kano ya ce ya karbi hayar akwatunan lefe ne saboda yana son yin auren amma kudaden sa ba za su is aba.

“Na karbi hayar akwatunan lefen ne saboda kudin lefe na ba zai isa har na sayi akwatin ba.

“Kuma matata bata taba ganewaba saboda naje na biya kudin da kandan kadan har na kammala biya” a cewar sa.

Shi kuwa wani mai sana’ar tuka baburin adai-daita Sahu Garzali Shu’ibu ya ce ya karbi hayar akwatunan kayan lefe da kayan a ciki baki daya.

“Na karbi hayar akwatunan lefe makare da kaya sai dai abin takaici matata ta bankado ni.

“Masu kayan suka dinga zuwa gidana saboda na kasa biyan su ban iya biyan kayan ciki ba balantan akwatunan.

“Haka kawai wata rana suka zo gidan suka gayawa matata komai.

“Baya da na dawo ne ta fara tambayata ya akayi na hada lefen da na kai mata?

“Hakan ya sanya rigimar yau daban ta gobe daban daga karsehe dai ta bar gidan.” Ya ce.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending