KANUN LABARAI
Shin da gaske ne maza na kukan aure?
Zulaiha Danjuma
kukan aure wani lamarine da aka saba gani ga mata musamman ma lokacin da aka dauke su za a kai su dakin mazajen su.
Sai dai wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ya nuna cewa dayawa maza ma na shan kuka lokacin bikin su.
A zantawar jaridar Kano Focus da wasu matasa a nan Kano sun ce tabbasa maza kan yi kukan aure bisa dalin shakuwa da uwa, numa farinciki, jin dadin mallakar amaryar da sauran su.
Shakuwa da uwa

Wani matashi a nan Kano Umar Faruq Musa da ke sana’ar daukan hoto ya ce ya sha ganin angwaye na rusa kuka ranar daurin auren su ko kuma awurin biki.
Ya ce wasu da ya gani suna irin wannan kukan tsananin shakuwa ce da mahaifiyar su ya sanyasu gurshekar kuka.
“Mun zo tafiya da shi domin kai shi dakin sa, nan take mahaifiyarsa ta fara kuka shima sai ya barke da kukan”
“A lokacin ma akwai wadanda suka nuna cewar yana namiji amma yake sheka kuka dan zai bar gida? Sai dai a fahintata shakuwa da uwa ba wasa bane.
“Suma masu fadar hakan watakia basu shakun bane kamar shi” a cewar sa.
Farin ciki
Haka zalika wani magidanci da ke unguwar Gaida a nan Kano Nafi’u Usman ya ce angwaye da dama na yin kuka dalin farin ciki.
A cewarsa wani angon bai taba tsammanin jama’a za su taru saboda shi ba, amma da ya waiga ya ga irin jama’ar da suka taro dominsa farinciki kan saka shi kuka.
“A fahintata abune da ya kamata, dai-dai ne ango ya sha kukan sa lokacin biki ba gazawa ba ne farin ciki ne.
Idan farin ciki ya cikawa mutum zuciya ba kowane zai iya dannewaba, tilas wani sai ya amayar an gani” a cewar sa.
Haka dai wani magidancin Injiniya Aliyu Ibrahim ya ce ya rarrashi angwaye da dama da suka sha kuka lokacin bikin su.
“Abokina da ya yi kuka a bikinsa ya yi ne sakamakon ganin abokanan arziki da suka halarci daurin auransa.
“Ya fara godewa jam’a ne kawai sai muka ga idanunsa na rawa, ba jimawa kawai sai muka ji ya barke da kuka” ya ce..
Wahalar samun mata
Wasu matasan sunce angwaye na yin kuka ne domin yi wa kai barka da samun matar.
A cewar su wasu mazan har ranar da za a daura musu aure suna shakkun ko matar mallakinsu ce ko kuma za su iya rasa ta.
A cewar Usman Sa’idu da kyar ya rarrashi abokinsa da ya fara kukan barka-barka.
“Abokina da kyar muka rarrasheshi, saboda yunkurin salwantar masa da amaryar da aka yi,
“Danginta suna ta son hadata da wani na dangi sai da kyar Allah ya kwato ya bashi.
“Ai kuwa ana kammala daurin aurenne ya samu wuri ya dinga rusa kuka abin sa saboda ya tabbatar ya kubuta.
Ko ya da ce aga ango na kuka?
Wasu ba’arin matasan sunce ko kadan bai da ce ba aga ango na kuka, la’akari da cewar mata aka sani da yin hakan.
A cewar Malam Sa’idu mazaunin unguwar Jakara a nan Kano namiji da karfin zuciya aka sanshi ba wai kawai saboda an daura masa aure ya kama kuka ba.
“A fahinta ta matukar namji ya fara da kuka tun daga ranar bikin sa to matarsa ta samu lagonsa .
“Haka kuma wadanda basu san dalilin kukan sa ba za su yi masa kallon kuriciya ne kawai” a cewar sa.
Ra’ayin mata
Sai dai daga bangaren mata kuma sun ce babu wani aibu dan namji ya yi kuka a bikin sa.
Rukaiyya Tijjani da ke sana’ar kwalliyar mata ta ce ko kadan babu abun kunya dan namaji ya sha kukan sa.
Ta ce wasu ma kafin aurensu sun shan yin kuka a gaban ‘yan matan su ballantana maganar aure.
Ta ce taga maza da suka yi kuka gaban yan matan su har kashi uku domin neman sasantawa bayan da suka samu matsala.
Sai dai a ra’ayin Khadija Sani Maitama tace, matukar taga namiji yana kuka ranar auren sa to za ta yi masa kallon dan soyayya ne kawai.
Ta ce dukakanin wanda ya aibunta namiji don ya yi kuka akan matar da yake so tabbas bai samu wadanda za su yi kuka a kansu ba ne.
Bai kamata namiji ya yi kuka ba
Wasu daga cikin matan ra’ayin su ya banbanta inda suka ce bai kamata namiji ya ya yi kuka ba sabo da kawai ana bikin sa
A cewar matashiya Rabi’a Namaradda bashi da ma’ana, a ga namiji na kuka a bikinsa.
“Gaskiya kamar ya bada kaine, wasu ma cewa za su yi angontama sai da yayi kuku a ranar”
“Na taba zuwa wata walima naga ango na kuka mutane suka fara bai dace ba, bai dace na miji yayi kuka ba”
“Kamar ya rage martabar sane na mazaje, kamar a cikin mazajen ya dawo na kasan ne kamar shi ba gwarzon namiji bane” a cewar ta.
Haka zalika Amira Sani da ke unguwar ciranci a nan Kano ta ce duk namijin da yayi kuka a bikin sa to ba shakka sakarai ne
“Gaskiya ina yiwa duk namijin da ya yi kuka a bikin sa kallon sakarai”
“kuka a wurin namiji saboda ana yi masa aure shashanci ne a ganina gaskiya”

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
