Connect with us

KANUN LABARAI

An yi Maulidin shan kaurin Annabi a Kano

Published

on

Nasiru Yusuf

A ranar Alhamis ne aka yi Maulidin shan kaurin Annabi Muhammad (SAW) a Masallacin Juma’a na Shehi Malam Karami dake Madinatul Karmawi, Kofar Waika anan birnin Kano.

An gabatar da Maulidin karkashin jagorancin Shehi Muhammad Nazifi Alkarmawi, inda aka gabatar da tarihin Annabi da mu’ujizozinsa da falalar son Annabi da kuma bin sunnarsa.

Shehi Muhammad Nazifi Alkarmawi ya shaidawa Kano Focus ya fara Maulidin ne shekaru takwas da suka wuce, kamar yadda Hausawa ke shan kauri idan an yi kwana biyar da haihuwa don girmama Annabi.

“Muna wannan Maulidi ne don girmama Manzon Allah da kuma murna da farinciki da haihuwarsa, da kuma dada godiyarmu ga Allah ta’ala da ya ba mu shi. Shi ne sirrin samuwar Annabi Muhammadu.

“Kullum mukan yi kira ga ‘yan uwa irin wannan abubuwa masu kyau su dinga koyi da shi in ana yi.

“Muna jin dadi wasu wurare dabam-dabam sun dauki wannan sunna ta shan kauri ga Manzon Allah ana ta yi.

“Wasu ma sukan ka gabatar ranar kwana hudu a sha, domin rana ta biyar a zauna.

“Wasu ma idan an yi na biyar din sukan gabatar a kwana na shida,” a cewar Malamin.

Shehi Muhammad Nazifi Alkarmawi ya kara da cewa a lokacin Maulidin akan sha romo da gurasa don faranta zukatan masoya Annabi.

Malamin ya cigaba da cewa “Ya inganta duk abun da aka tattala na wajen Maulidin Annabi ko aka yi wani taro don girmama Manzon Allah, to abun da duk aka kawo a wurin na ci, ko na sha, wanda duk ya ci da niyyar  abun nan na Manzon Allah ne, to ya inganta Allah Tabaraka wa Ta’ala ya na gafarta zunubbansa kamar sannan babarsa ta haife shi.

“Shi ya sa mukan ce: su kantu, Gurasa fa duk mun aje su, a wanna wurin don isar Maulidi.

“Dabino da soye duk mun aje su.

“Duk abin da aka ba ka kar6i ka ci don a sami wannan albarka. “Muna tabbatar da cewa wanda ya ci abun wurin hidimar Annabi na walima da Maulidin nan, to ai ko da a gidan ma ba a ci ba, ka ci ka je kana kamshi wanda ma ya ji kamshin shi ma an gafarta masa.”

Taron Maulidin ya samu halartar manyan malamai da limaman masallatan Juma’a daga sassa daban-daban na jihar Kano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending