Connect with us

KANUN LABARAI

Ko jam’iyyu a Kano za su baiwa matasa dama a zabukan da ke tafe

Published

on

Aminu Abdullahi

Matasa a jihar Kano sun koka kan yadda siyasar uban gida da kudi ke neman kassara musu mafarkin su na zama zababbu a matakai daban daban na shugabancin kananan hukumomi dake tafe.

Jaridar Kano Focus tayi nazari kan yadda matasa daga kananan hukumomi daban daban suka fito don ganin an zabe su a kujerar shugabancin karamar hukuma ko ta kansila.

A baya dai ba safai aka saba ganin matasan na tsayawa takara ba, yayin da kuma wasu ke shan kayi tun a zaben fidda gwani na cikin gida, wasu kuma akan nemi da ayi sulhu domin janyewa wadanda suka dara su shekaru kuma suke da abin hannu.

Nuradeen Babani Musa mai shekaru ashirin da biyar dake takarar shugabancin karamar hukumar Tudun Wada a jam’iyyar A.P.C ya ce  rashin isassun kudade da iyayen gida yasa tun a zaben fidda gwani da jam’iyu ke gudanarwa ake watsi dasu.

Ya ce wani lokacin akan tilasta musu da su janyewa wadanda shekarun su sukaja kuma suke da abin hannu.

Ya kara da cewa barin matasa da ‘yan siyasa suke yi a baya shiyasa ya fito takarar shugabancin karamar hukumar amma kuma da alama gwamnati tana da wanda takeso ya tsaya takarar.

“Akwai matasa da yawa da muka fito takarar tare dasu, akwai kuma manya masu shekaru da kudi, da alama kuma a cikin manyan za a bawa wani takarar.

“Yawanci wadanda suka haura shekaru hamsin ne ke tsayawa takarar, yanzu mun fito za a yi zaben fidda gwani amma alamu na nuna cewa jam’iyya nada wadanda suke so,” inji shi.

Haka zalika wani dan takarar Kansila a karamar Hukumar Rano a jam’iyyar A.P.C mai shekaru ashirin da biyar Usman bn Usman cewa yayi bai kamata manyan da suka haura shekaru talatin su  fito takara a kananan hukumomi ba.

Yana mai cewa kamata ya yi su zama masu bada shawara kawai ga matasa kasancewa suma matasa na da rawar da za su taka don kawo canji a cikin al’umma.

Sai dai ya ce da yawa idan matasa suka fito takara akan nemi da ayi sulhu da su,  ba tare da an gudanar da zaben cikin gida ba.

Zaben Kananan hukumomin Kano zai lakume sama da Naira miliyan dubu biyu

Za mu bada cikakken tsaro yayin zaben kananan hukumomi a Kano-Kwamishinan ‘yan sanda

Rashin filayen wasanni na kara sanya yara da matasa zama dakikai a Kano

Ya kara da cewa jam’iyar da yake takara bata barin kowa yasiyi fom na tsayawa takarar fidda gwani a karamar hukumar Rano, maimakon haka sai dai jam’iya tayi sulhu a tsakanin ‘yan takara tare da siyawa wanda aka zaba fom din tsayawa.

“Jam’iyya tana yaudarar ‘yan takara ne ta hanyar cewa sulhu alkairi ne daga nan kuma sai a zabo bara gurbi a dora wanda ba zai yiwa al’umma komai ba.

“Kaga a mazabarmu sulhun ma gagara ya yi karshe jam’iya ce kawai ta dauko wanda takeso tace yayi takara,” a cewar sa.

Nura Abdullahi mai shekaru ashirin da uku dake takarar kansila a tsohon gari dake karamar hukumar Tudun Wada a jam’iyyar P.D.P ya ce akwai alamun cewa jam’iyyar sa za ta tsaida shi a matsayin dantakarar kansila.

Ya ce duk da rashin kudi isassu ga matasa amma a wannan karon alamu na nuna cewa za a samu matasa cikin shugabancin karamar hukuma dana kansiloli.

Nura Abdullahi ya kara da cewa matukar aka baiwa matasa dama to tabbas za su kawo canji kan yadda ake tafiyar da tsarin kananan hukumomi a jihar nan.

Gwamnati ke yin nune

Shugaban jam’iyyar A.P.C dake mazabar Rano ta tsakiya a karamar hukumar Rano Mukhtar Dahiru yace ko kadan shugabanin jam’iyya basa hana matasa tsayawa zaben fidda gwani.

Ya ce masu mulki dake da ruwa da tsaki a gwamnati suke yin uwa da makarbiya ga zabukan kananan hukumomi domin kuwa suke nuna wanda suke so ya tsaya takara.

Ya kara da cewa a karamar hukumar Rano dan majalisar jihar na tarayya Kabiru Alhassan Rurum shike nuna wanda za a tsayar a matsayin kansila ko shugaban karamar hukumar yankin.

Mukhtar ya kuma cewa dabi’ar nune da dan majalissar keyi yasa duk wanda aka zaba a matsayin shugaban karamar hukuma ko kansila basa ganin shugabannin jam’iyyu da kima.

“Wani lokacin ma ba ayin sulhu kawai wani babba a gwamnati ne zaice ga wanda yake so kuma ba yadda za a yi shi za a tsayar a matsayin dan takara na jam’iyya,” a cewar sa.

Sulhu muke yi

Ya yin zantawar sa da jaridar Kano Focus mai rikon shugabancin jam’iyyar PDP na jihar Kano Danladi Umar Abdulhamid cewa ya yi jam’iyyar PDP bata yin nune.

Ya ce hasalima jam’iyya ce dake baiwa matasa maza da mata dama don su nuna tasu kwarewar a siyasance domin ciyar da kasa gaba.

Ya kara da cewa suna gudanar da zaben fidda gwani ga duk kan ‘yan takara sannan wanda yaci sai bashi.

Saidai wani lokacin sukan yi sulhu ga ‘yan takarar don rage musu kashe kudi.

“Wani lokacin idan aka samu akayi sulhu tsakanin juna yakan fimana sauki a matsayin mu na yan adawa saboda kada dan adawa ya kashe kudi kuma idan yaci jam’iyya mai mulki ta hana shi.

“A matsayina na shugaban jam’iyya a yanzu ina iya yimaka rantsuwa banda wani dan takar,  hakama yan kwamitina na yi zama dasu sunyimin rantsuwa cewa basu da wani dan takara a da zasu nuna,” a cewar sa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina

Published

on

 

Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.

 

Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.

 

Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.

 

Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).

 

“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.

 

Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.

 

“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.

Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.

 

“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.

 

Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Trending