KANUN LABARAI
Ko jam’iyyu a Kano za su baiwa matasa dama a zabukan da ke tafe
Aminu Abdullahi
Matasa a jihar Kano sun koka kan yadda siyasar uban gida da kudi ke neman kassara musu mafarkin su na zama zababbu a matakai daban daban na shugabancin kananan hukumomi dake tafe.
Jaridar Kano Focus tayi nazari kan yadda matasa daga kananan hukumomi daban daban suka fito don ganin an zabe su a kujerar shugabancin karamar hukuma ko ta kansila.
A baya dai ba safai aka saba ganin matasan na tsayawa takara ba, yayin da kuma wasu ke shan kayi tun a zaben fidda gwani na cikin gida, wasu kuma akan nemi da ayi sulhu domin janyewa wadanda suka dara su shekaru kuma suke da abin hannu.
Nuradeen Babani Musa mai shekaru ashirin da biyar dake takarar shugabancin karamar hukumar Tudun Wada a jam’iyyar A.P.C ya ce rashin isassun kudade da iyayen gida yasa tun a zaben fidda gwani da jam’iyu ke gudanarwa ake watsi dasu.

Ya ce wani lokacin akan tilasta musu da su janyewa wadanda shekarun su sukaja kuma suke da abin hannu.
Ya kara da cewa barin matasa da ‘yan siyasa suke yi a baya shiyasa ya fito takarar shugabancin karamar hukumar amma kuma da alama gwamnati tana da wanda takeso ya tsaya takarar.
“Akwai matasa da yawa da muka fito takarar tare dasu, akwai kuma manya masu shekaru da kudi, da alama kuma a cikin manyan za a bawa wani takarar.
“Yawanci wadanda suka haura shekaru hamsin ne ke tsayawa takarar, yanzu mun fito za a yi zaben fidda gwani amma alamu na nuna cewa jam’iyya nada wadanda suke so,” inji shi.
Haka zalika wani dan takarar Kansila a karamar Hukumar Rano a jam’iyyar A.P.C mai shekaru ashirin da biyar Usman bn Usman cewa yayi bai kamata manyan da suka haura shekaru talatin su fito takara a kananan hukumomi ba.
Yana mai cewa kamata ya yi su zama masu bada shawara kawai ga matasa kasancewa suma matasa na da rawar da za su taka don kawo canji a cikin al’umma.
Sai dai ya ce da yawa idan matasa suka fito takara akan nemi da ayi sulhu da su, ba tare da an gudanar da zaben cikin gida ba.
Zaben Kananan hukumomin Kano zai lakume sama da Naira miliyan dubu biyu
Za mu bada cikakken tsaro yayin zaben kananan hukumomi a Kano-Kwamishinan ‘yan sanda
Rashin filayen wasanni na kara sanya yara da matasa zama dakikai a Kano
Ya kara da cewa jam’iyar da yake takara bata barin kowa yasiyi fom na tsayawa takarar fidda gwani a karamar hukumar Rano, maimakon haka sai dai jam’iya tayi sulhu a tsakanin ‘yan takara tare da siyawa wanda aka zaba fom din tsayawa.
“Jam’iyya tana yaudarar ‘yan takara ne ta hanyar cewa sulhu alkairi ne daga nan kuma sai a zabo bara gurbi a dora wanda ba zai yiwa al’umma komai ba.
“Kaga a mazabarmu sulhun ma gagara ya yi karshe jam’iya ce kawai ta dauko wanda takeso tace yayi takara,” a cewar sa.
Nura Abdullahi mai shekaru ashirin da uku dake takarar kansila a tsohon gari dake karamar hukumar Tudun Wada a jam’iyyar P.D.P ya ce akwai alamun cewa jam’iyyar sa za ta tsaida shi a matsayin dantakarar kansila.
Ya ce duk da rashin kudi isassu ga matasa amma a wannan karon alamu na nuna cewa za a samu matasa cikin shugabancin karamar hukuma dana kansiloli.
Nura Abdullahi ya kara da cewa matukar aka baiwa matasa dama to tabbas za su kawo canji kan yadda ake tafiyar da tsarin kananan hukumomi a jihar nan.
Gwamnati ke yin nune
Shugaban jam’iyyar A.P.C dake mazabar Rano ta tsakiya a karamar hukumar Rano Mukhtar Dahiru yace ko kadan shugabanin jam’iyya basa hana matasa tsayawa zaben fidda gwani.
Ya ce masu mulki dake da ruwa da tsaki a gwamnati suke yin uwa da makarbiya ga zabukan kananan hukumomi domin kuwa suke nuna wanda suke so ya tsaya takara.
Ya kara da cewa a karamar hukumar Rano dan majalisar jihar na tarayya Kabiru Alhassan Rurum shike nuna wanda za a tsayar a matsayin kansila ko shugaban karamar hukumar yankin.
Mukhtar ya kuma cewa dabi’ar nune da dan majalissar keyi yasa duk wanda aka zaba a matsayin shugaban karamar hukuma ko kansila basa ganin shugabannin jam’iyyu da kima.
“Wani lokacin ma ba ayin sulhu kawai wani babba a gwamnati ne zaice ga wanda yake so kuma ba yadda za a yi shi za a tsayar a matsayin dan takara na jam’iyya,” a cewar sa.
Sulhu muke yi
Ya yin zantawar sa da jaridar Kano Focus mai rikon shugabancin jam’iyyar PDP na jihar Kano Danladi Umar Abdulhamid cewa ya yi jam’iyyar PDP bata yin nune.
Ya ce hasalima jam’iyya ce dake baiwa matasa maza da mata dama don su nuna tasu kwarewar a siyasance domin ciyar da kasa gaba.
Ya kara da cewa suna gudanar da zaben fidda gwani ga duk kan ‘yan takara sannan wanda yaci sai bashi.
Saidai wani lokacin sukan yi sulhu ga ‘yan takarar don rage musu kashe kudi.
“Wani lokacin idan aka samu akayi sulhu tsakanin juna yakan fimana sauki a matsayin mu na yan adawa saboda kada dan adawa ya kashe kudi kuma idan yaci jam’iyya mai mulki ta hana shi.
“A matsayina na shugaban jam’iyya a yanzu ina iya yimaka rantsuwa banda wani dan takar, hakama yan kwamitina na yi zama dasu sunyimin rantsuwa cewa basu da wani dan takara a da zasu nuna,” a cewar sa.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
