KANUN LABARAI
‘Yan sanda a Kano sun kama dan sahun da ke sauke fasinja ya gudu da kayansu
Aminu Abdullahi
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wani direban adai-daita sahu mai suna Muhammad Muhmmad bayan da ya tsere da kayan fasinjoji.
Kano Focus ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a unguwar Na’ibawa ‘yan Lemo a ranar Litinin.
Hadiza Hashim wacce dan sahun ya tserewa da kayan ta ce dan sahun ya shammace ta ne ya kuma gudu da kayan da ta yi cefane.
Kayan su hadar da buhun fulawa da katan din taliya da magi da kuma shaddoji da yaduka.

Ta ce direban adaidaita sahun ya kashe baburin nasa ne da sunan ya mutu a daidai lokacin da suka isa gadar Na’ibawa mai hawa uku.
Sai dai ta ce lokacin da ya ce su sauka domin ya duba me ya kashe masa baburin sai tayi kokarin haddace lamabar da ke jikin baburin.
“Ya nemi mu tura masa baburin, sai da muka tura masa ne ya shiga da gudu ya kunna abinsa ya wuce ya barmu nan tsaye.
“Amma lokacin da yace mu sauka nayi sauri na rike Lambar baburin nasa.
“Bakar nambar itace 6543 Gwale yayinda kuma plate nambar sa itace Adamawa Yola 194 QA.
“Lokacin da ya gudu sai nayi salati sai kuma naji wani huci mai zafi ya lullube ni daga nan kuma bansan inda kaina yake ba.
“A she suma nayi daga nan kuma sai mai gidana yazo ya dauke ni ya kaini asibiti,” a cewar ta.
Muhammad Ahmad Muhammad shi ne direban adai-daita sahun da ya ce son zuciya ne yasa ya aikata abinda ya yi sai dai ya yi matukar nadama.
Muhammad mai shekaru talatin da tara mazaunin unuguwar Kabuga ya ce bayan da ya gudu da baburinne sai kuma jami’an ‘yan sanda suka bibiyi nambar baburin.
Hakan ta sanya suka kama kaninsa sa’ilin da yake aiki da baburin wanda daga nanne aka kama shi.
Ya ce lokacin da aka kamashi ya riga ya siyar da fulawa da taliya sannan kuma ya kai a jiyar ragowar kayan gurin abokin sa.
“Yanzu duk an kamomu dani da kuma wanda na kaiwa a jiyar ragowar kayan.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce jami’ansu ne suka yi bincike saka kuma kamashi.
Kiyawa mai mukamin mataimakin sufurtandan ‘yan sanda ya ce tuni aka kammala bincike kuma za su gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
