Connect with us

KANUN LABARAI

Yanayin sanyi: Hadarin da ke tattare da sana’ar wanki a Kano

Published

on

Aminu Abdullahi

Wani kwararen likita a nan Kano Dr Bashir Bala Getso ya ce masu sana’ar wanki a lokacin sanyi na cikin hadarin kamuwa da cutuka masu hadarin gaske.

Kano Focus ta ruwaito Dr Bala Getso wanda shi ne shugaban kwalejin kula da lafiyar muhalli ta jihar Kano ya ce masu sama’ar za sui ya kamuwa da cutukan da suka hadar da ciwon sanyin kashi da nimoniya, ciwon kafa da kuma ciwon sikila.

Bala Getso ya ce kowanne dan adam akwai yadda jikinsa  ke karbar yanayi.

Ya kara da cewa masu sana’ar wanki ka iya kamuwa da cututtuka da kan dauki lokaci ba tare da an fahimce sub a ma baki daya..

Haka zalika akwai wasu cututuukan da kan tsahi sakamon yadda suke mu’amila da ruwa a koda yaushe da suka hada da ciwon sikila da nimoniya.

Malam Getso ya kuma ce wajibine masu sana’ar wanki su rage yawan lokutan da suke dauka suna yin wanki.

“I dan sunayin wanki kamar ranaku biyar a sati to kamata ya yi su mai dashi ranaku uku.

“Haka kuma idan suna yin wankin a wa biyar a rana kamata ya yi su rage awanni don kare lafiyar su,” a cewar sa.

Ya kara da cewa ga wadanda sana’ar ta zame musu dole musamman ma wadanda ke aiki a bakin rafi to kamata yayi su dinga bari sai rana ta fito.

Ya kuma ce yana da kyau a irin wannan yanayi na sanyi masu sana’ar wanki su rinka ziyartar likitoci domin samun shawarwari kan yadda za su kare kansu daga illolin da yanayin sanyi ke tafe dasu.

Suma masu sana’ar wakin da jaridar Kano focus ta zanta da su sun ce suna yin la’akari da yanayin na sanyi wajen kare lafiyar su.

Abdulrashid Ibrahim dake sana’ar wanki a unguwar Sharada ya ce kafin shigowar sanyi yana fara  sana’ar sa ne da misalin karfe shida na safe.

Amma yanzu saboda yanayin da ake ciki yakan bari rana ta fito sosai kamar karfe daya kafin ya fara.

Ya kuma ce farashin da yake yin wanki bai sauyaba dukkuwa da yanayin sanyin da ake ciki.

“Ina wanke riga da wanda ko da zani naira dari biyu idan za a saka sitati, idan kuma Babu sitati to naira dari da hamsin nake karba,” a cewar sa.

Malam Ibrahim ya ce baya zuwa asibiti domin a duba lafiyar sa amma duk inda yaji ana saida maganin gargajiya da ya shafi cutar sanyi to yana siya yayi amfani dashi.

Shima wani mai wanki Sa’idu Sulaiman dake unguwar Gwale Sani Mainagge ya ce duk da yanayin sanyin da ake ciki amma bai kara farashin kudin wanki ba.

Ya ce akwai masu wanki sosai da idan ya kara kudin masu kawo masa wanki za su koma kaiwa wasu daban.

Haka zalika ya ce yana sa rigar sanyi da safa ta hannu da kafa don kare kansa daga ciwon sanyin kasancewar illar sanyi kan dade a jikin mutum.

“Bamu da gida a nan kusa hakan tasa bama samun damar sirkawa da ruwan dumi,” a cewar sa.

Shi ma wani mai suna Shamsu Ibrahim dake unguwar Gwale ya ce suna shan wahala sosai lokacin sanyi.

Ya ce har yanzu bai canza lokacin da yake fara sana’ar sa ba , a cewarsa karfe shida yake farawa.

Ya kuma ce rashin kungiya tasa kullum masu wanki ke zama koma baya a cikin masu yin kananan sana’o’i a jihar nan.

Ya ce akwai bukatar kungiyoyi da gwamnati su rinka tallafawa masu sana’ar wanki da magunguna duba da irin halin da suke tsintar kansu a lokutan sanyi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Trending