KANUN LABARAI
NLC ta ja kunnen Ganduje kan zabtare albashin ma’aikata

Aminu Abdullahi
Kungiyar kwadago ta kasa ta bukaci gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da ya dakatar da zabtare albashin ma’aikatan Kano don kaucewa barkewar rikicin ma’aikata.
Kano Focus ta ruwaito wannan na kunshene cikin wata wasika da kungiyar ta aikewa gwamnan mai dauke da sa hannun shugabanta Kwamared Ayuba Wabba ranar Laraba.
Ta cikin wasikar kunigiyar ta bukaci da a mayarwa da ma’akatan da aka zabtarewa kudadensu cikin gaggawa.
NLC ta kuma ja hankalin gwamnatin da ta biya mafi karamcin albashi na naira N30,000 kamar yadda doka ta tanada.

“Muna neman a dakatar da rage albashin da ake biyan ma’aikatan jihar Kano batare da bata lokaci ba.
“Muna kuma bukatar Gwamnatin Jihar Kano ta sauke nauyin da ke kanta na biyan sabon mafi karancin albashi na N30,000.”
Ganduje ya zaluncemu miliyan 80 a albashin Nuwamba da Disamba-ma’aikatan kotu
Ganduje ya zabtarewa ma’aikatan Kano albashi
Ganduje ya zabtarewa ma’aikatan Kano albashi
NLC ta ce tayi takaici kan yadda gwamnantin ta tsayar da biyan ma’aikata mafi karancin albashi duk kuwa da cewa itace jiha ta farko data fara yin biyayya ga dokar Karin mafi karancin albashin.
Haka kuma kungiyar ta NLC ta ki amincewa da dalilan da gwamnati ta bayar na rage albashin ma’aikata.
A cewarta ikirarin da tayi na cewa tabarbarewar tattalin arzikin da cutar KORONA ta haifarne ya jawo zabtare kudaden ma’aikata da jefasu halin kaka nikayi ba gaskiya bane.
Wabba ya ce in har akwai lokacin da za a karawa ma’aikata albashi to bai wuce yanzu ba da annobar KORONA tayi musu illa.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
