Connect with us

KANUN LABARAI

‘Yan bindiga sun kashe shugaban karamar hukuma a jihar Taraba

Published

on

Abdullahi Musa

Wasu ‘yan bindiga da ba a kai ga tantance ko su waye ba sun kashe shugaban karamar hukumar Ardo-Kola da ke jihar Taraba, Salihu Dovo.

Kano Focus ta ruwaito kisan nasa ya biyo bayan saceshi da yan bindigar suka yi a safiyar ranar Lahadi a gidansa da ke Unguwar Sabon Gari a Jalingo, babban birnin jihar.

A cewar danginsa ‘yan bindigar sun tafi da shugaban karamar hukumar zuwa wani boyayyen wuri.

Bayan ‘yan sa’o’i kadan ne kuma aka kira danginsa domin su zo su dauke gawarsa a cikin daji.

A cewar majiyar, mutanen wadanda yawansu ya kai kimanin 20 sun shiga ta katangar gidansa, suka kuma farwa jami’an tsaro kafin su samu shiga cikin gidan.

Yadda kawuna ya turoni Kano domin garkuwa da mutane

Rundunar ‘yan sandan Kano ta kubutar da attajirin Minjibir da aka yi garkuwa da shi

Rundunar ‘yan sandan Kano ta kubutar da attajirin Minjibir da aka yi garkuwa da shi

Kafin su tafi da shugaban karamar hukumar, majiyar da ke gidan lokacin da lamarin ya faru, ta ce ‘yan bindigar sun kuma yi awon gaba da wasu wayoyinsu na hannu.

Haka kuma yan bindigar ko kadan basu nemi kudin fansaba, ballantana a sa ran sakoshi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar David Misal ya fada wa manema labarai a wayar tarho cewa an cafke mutane biyu da ake zarigin suna da hannu a kisan.

Haka zalika tuni aka fara bincike don ci gaba da gano wadanda suka aikata wannan mummunar dabi’ar.

Tuni dai aka dauki gawar zuwa dakin ajiye gawa da ke asibitin  Federal Medical Center Jalingo.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending