KANUN LABARAI
Gwamnati ta fara gididdiba gidan rediyon Kano

Aminu Abdullahi
Gwamnatin Kano ta fara aiwatar da shirinta na yanka filaye a cikin gidan rediyo manona da ke unguwar tukuntawa da ke karamar hukumar Birni da ya shafe sama da shekaru 40.
Kano Focus ta ruwaito wannan na nuna cewa mutane sama da 1000 za su rasa sana’arsu da sukeyi a gidan
Al’umma da dama ne ke gudanar da sana’ar noman lambu a cikin gidan radiyon, inda kuma aka basu wa’adin tashi kafin shukarsu ta nuna.
An rushe dakunan yada labarai

A binciken da Kano Focus ta gudanar ta gano yadda aka rushe dakin watsa labarai dake cikin gidan rediyon, tare da sauke doguwar area dake watsa labarai.
Haka zalika an fara fitar da filotai a filin gurin wanda wata majiya tace za a fitar da filotai guda dari shida tare da fara rushe wani bangare na katangar da ta kewaye gidan rediyon.
Munyi asarar shukarmu
Danlami Muntari mai shekaru 55 ya ce da suna jin jita-jitar za a tashe su amma yanzu suka gasgata.
Ya ce masu aikin gurin sun basu sati biyu ne kawai su tashi, ya yin da galibi daga cikin masu shuka a wurin, sai nan da wata uku amfaninsu zai nuna.
Ya kara da cewa tun yana yaro karami ake zuwa dashi noman lambu a cikin gidan rediyon, har ya girma shima ya fara sana’ar ta lambu sai gashi rana tsaka za a tashe su, ba tare da sanin makomar su ba.
“A zahirin gaskiya ba wata sana’a da nasani fiye da wannan, kuma irina suna da yawa.
“Amma ba wani shiri da akayi na sauya mana wani wurin, kuma mun shigar da korafinmu, amma har yanzu shiru kakeji, sai muyi addu’a allah ya yi mana zabi nagari.
“Ko da ba za a sauya mana wani gurin ba, yakamata a cikin fulotan muma a sanmana wasu wuraren a ciki,” a cewar sa.
Ba a sanarda mu za a yanka filaye ba
Adamu Sule mai shekaru 80 da ya shafe shekaru 60 yana sana’ar lambu ya ce ba wata sanarwa da suka samu, kawai dai sun wayi gari sunga ana aiki a cikin gidan rediyon.
“A nan nake yini, kullum da safe idan nafito nan nake zuwa inayin aikin lambu, kaga yanzu sai dai na koma gida tunda babu abinda na iya inba aikin lambu ba,” inji Adamu.
Gadon iyayenmu ne za a kwace
Dauda Balarabe dan shekara 40 ya ce sun kafa kwamiti da suka je gidan Gali Umar Na’abba don mika korafinsu, har yanzu ba wani abu da aka yi musu.
Ya kara da cewa shekara da shekaru suna samun na cin abinci a gurin, amma rana tsaka ance sutashi, wanda a yanzu basu san makomar suba.
Wani mai suna Garba Bala mai shekaru 65 ya ce sun gaji filayen gidan rediyonne a gurin kakanninsu, don kuwa shima a wancan lokacin naira dari shida ya siyi nasa filin a ciki.
Ya ce kaso 90% na mutanen da ke sana’a a wurin basu da madogara matukar aka tashesu batare da an sauya musu wani wurin ko an tallafa musu ba.
Amayarda wurin makabarta
Saidai kuma wasu daga cikin al’ummar dake yankin gidan rediyon sun bayyana mabanbanta ra’ayoyi kan matakin rushe gidan rediyon.
Sulaiman Kabiru ya ce fatansu ga gwamnati shi ne ta samar musu da makabarta a cikin fulotan da zata yanka a gurin.
A cewarasu al’umma gidan maza da sabuwar gandu na fama da rashin makabarta.
“Munyi maraba gaskiya da tashin wannan guri da za ayi, sai dai muna so gwamnati ta yiwa al’ummar wannan unguwa wani abu da zasu amfana,” a cewar sa.
Muhsin Lawan ya ce sau tari idan batagari suka yi sata da zarar sun haura gidan shikenan sun sha.
Sai dai ya ce yana fatan gwamnati za ta tallafawa wadanda suka dauki shekaru masu yawa suna neman abinci a wurin, tare da samarwa al’ummar yankin makaranta.
“Gaskiya bana goyan bayan yanka filaye a wannan wuri duba da yadda gurin ke daya daga cikin gurararen da a jihar Kano ke samar da kayan lambu.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
