KANUN LABARAI
Gwamnatin tarayya ta amince a bude sabbin jami’o’i uku a Kano
Mukhtar Yahya Usman
Gwamnatin tarayya ta amince a bude sabbin jami’o’i uku masu zaman kansu a Kano.
Kano Focus ta ruwaito gwamnatin ta amince a bude jami’o’in a zaman majalisar zartarwa na kasa ranar Laraba.
Haka kuma gwamnati ta amince da bude wasu jami’oin goma sha bakwai a sauran sassan kasar nan.
Jami’o’in da aka amince su fara aiki a Kano sun hadarda Jami’ar Maryam Abacha da kuma Jami’ar Capital City, sai kuma Jami’ar Al-Istiqama, a karamar hukumar Sumaila.

Sauran sun hadarda Jami’ar Top faith dake, Mkpatak, a jihar Akwa Ibom, sai Jami’ar Thomas Adewumi dake garin Oko-Irese a jihar Kwara da kuma jami’ar Maranathan a jihar, Imo da jami’ar Ave Maria a jihar Nasarawa State.
Haka kuma Sauran sun hadar da jami’ar Mudiame a jihar Edo da Havilla Nde-Ikom, a jihar Cross River sai jami’ar Claretian a jihar Imo, sai jami’ar NOK da ke Kachia, a jihar Kaduna da kuma Karl-Kumm a jihar Filato.
Covid-19-Gwamnatin Kano ta rufe asibitin UMC Zahir dake Jambulo
Maganin gargajiya ya yi sanadiyyar mutuwar yara biyu a Kano
KANSIEC na neman cinye mana hakkokinmu-jami’an zaben kananan hukumomi
A cewar ministan Ilimi Malam Adamu Adamu dukkan jami’o’in an basu ikon farawa a matakin gwaji na tsahon shekaru uku.
Haka kuma ya ce ma’aikatar Ilimi ta kasa ce za ta dinga bibiyarsu ta tantance kokarinsu kafin a basu lasisi na din-din-din.
Da wannan ne kuma jami’o’I masu zaman kansu a kasar nan suka kai 99

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
