Connect with us

KANUN LABARAI

Lafiya jari:Ko mene ne alaƙar cin goro da hawan jini

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Goro ɗan itaciya ne da ake amfani da shi domin ci, haka nan alama ce ta karrama baƙo yayin bukukuwa da sauran taruka, musamman a al’adun Najeriya da sauran ƙasashen Afrika ta yamma.

Bugu da ƙari ana amfani da shi a abubuwan sha domin ƙarin ɗanɗano.

Goro na ɗauke da sinadarai da dama da ake alaƙanta su da amfani kamar haka

Wartsakarwa: masu cin goro na amfani da shi domin wartsakewa, ƙara kuzari ko karsashi.

Maganin bacci ko kasala: saboda sinadarin kafin (caffeine) goro na iya rage jin bacci ko kasala.

Maganin tashin zuciya: ana amfani da goro domin magance matsalar tashin zuciya, musamman mata.

Dankwafe sha’awar abinci: Cin goro yayin jin yunwa na da tasirin rage sha’awar cin abincin ko jin matsananciyar yunwa.

Sauran amfanin goro da ke da alaƙa da lafiya

Rage raɗaɗin ciwon ɓarin kai (migraine).

Kashe ƙwayayyakin cuta a jiki.

Taimakawa masu ciwon asma(asthma) wajen buɗe hanyoyin numfashi.

Sai dai duk da waɗannan alfanu da bincike ke alaƙanta goro da shi, bincike ya nuna cewa; baya ga sauran sinadaran da ke cikin goro, goro na ɗauke da sinadarin kafin(caffeine) kaso 2 – 3 cikin ɗari.

Kuma bincike ya yi nuni da hauhawar jini bayan cin sinadarin kafin da ke cikin goro.

Sai dai hauhawar jinin ya fi ƙarfi ga masu cin goron a karon farko ko kuma masu ci jifa-jifa.

Haka nan hauhawar jinin zuwa na wani ɗan lokaci ne da sinadarin kafin zai ƙare a jiki.

Amma waɗanda suka shafe shekara da shekaru suna cin goron, jiki kan jure tasirin sinadarin kafin yau da gobe.

Saboda haka tasirin sinadarin kafin a kan hauhawar jini na raguwa ne da tsawon lokacin da aka daɗe ana amfani da shi.

Sai dai kuma wani bincike ya sake yin nuni da cewa ga masu hawan jini; amfani da goro yayin da ake shan magungunan hawan jini na da tasirin rage aikin maganin, musamman jinsin maganin hawan jini da ke rufe hanyar kalsiyam(Calcium channel blockers) wanda ke taimakawa wajen buɗa hanyoyin jini.

Bayan goro, sinadarin kafin na nan a cikin kofi(coffee), lemukan roba/gwangwani da baƙin shayi, har da ma wasu magungunan ciwo kai, mura, da kasala da ake saye a kasuwa.

Mafi kyawun al’amari tsakatsakinsa, saboda haka zai fi kyau a yi amfani da goro yayin buƙata kaɗai, amma ba ya zama ɗabi’ar kullum ba.

Sannan ga masu hawan jini, saboda hauhawar jini da sinadarin kafin ke kawowa, da kuma dankwafe tasirin jinsin wancan maganin hawan jini, zai fi kyau su ƙaurace wa cin goro, da sauran abubuwan da ke ɗauke da sindarin kafin.

Wannan bayani ba zai zamo a madadin tuntuɓar likitan ka/ki ba dangane da cin goro ko kafin.

 

Wannan bayani Kano Focus ta kwafo ne daga shafin Physiotherapy Hausa, mallakar asibitin koyarwa na Abdullahi Wase da ke nan Kano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina

Published

on

 

Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.

 

Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.

 

Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.

 

Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).

 

“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.

 

Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.

 

“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.

Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.

 

“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.

 

Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Trending