KANUN LABARAI
Yanzu-yanzu: An sulhunta tsakanin jami’an KAROTA da ‘yan Adai-daita Sahu
Mukhtar Yahya Usman
Biyo banyan zaman gaggawa da aka gudanar tsakanin jami’an KAROTA da kungiyar kwadago da kuma wakilan ‘yan adai-daita an cimma matsaya mai kyau.
Kano Focus ta ruwaito shugaban kungiyar Kwadago na jihar Kano kwamared Kabiru Ado Munjibir ne ya sanar da hakan yayin taron manema labarai ranar Talata a Kano.
Kabiru Ado Minjibir ya ce an cimma matsaya masu tarin yawa da za su taimaka gaya wajen kawo karshen halin da ake ciki.
Matsayar da aka cimma
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2022/02/KANO-ONLINE-ENGLISH.jpg)
‘Yan Adai-daita Sahu za su biya harajin N100 kamar yadda doka ta tanada a kullum amma ba kamar yadda ya ke a bayaba.
Duk wanda zai biya harajinsa to dole ne ya yi Remiter karon farko domin a dauki bayanan sa a adana.
Haka kuma kowanne dan sahu zai biya, na farko a tsakanin makonnin biyu daga ranar 23 ga Fabrairu.
Haka kuma bayan anyi biyan farko za a ci gaba da biya na kullum-kullun ta wayar hannu ko kuma ta POS ba kamar a baya ba da sai anje banki.
Haka kuma duk wanda ya ke so zai iya biyan na kwana daya ko na sati ko kuma na wata-wata ko na shekara amma ba dole bane.
Haka kuma yana dag cikin abinda aka cimma, cewar shugabannin masu dan sahu za su yiwa mambobinsu bayani kuma za a janye yajin aiki.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2023/04/NCC-aDVERT--208x300.png)
Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2024/11/Northwest-University-Kano.jpg)
Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2022/02/KANO-ONLINE-ENGLISH.jpg)
Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2023/04/NCC-aDVERT--208x300.png)
Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2024/10/IMG_8785.png)
Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2022/02/KANO-ONLINE-ENGLISH.jpg)
Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2023/04/NCC-aDVERT--208x300.png)
Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240704-WA0016.jpg)
Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2022/02/KANO-ONLINE-ENGLISH.jpg)
Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
![](https://kanofocus.com/wp-content/uploads/2023/04/NCC-aDVERT--208x300.png)