Connect with us

KANUN LABARAI

Da gan-gan gwamnati ta ki biyan kudin NECO-Iyayen yara

Published

on

Aminu Abdullahi
Iyayen yara da dalibai na cigaba da kokawa bisa yadda gwamnatin jihar Kano ta gaza biyan kudin jarabawar kammala karatun sakandire (NECO) da dalibai suka rubuta a watannin baya.
Kano Focus ta ruwaito cewa tun a watan Janairun shekarar da muke ciki ne a ka saki jarabawar  ta (NECO)  ta makarantu masu zaman kansu, sai dai sakamakon daliban makarantu gwamnati ya gaza fita a jihar nan.
Wani mahaifi mai suna Abubakar Isma’il da yaron sa ya rubuta jarabawar a makarantar sakandire dake Sabuwar Kofar ya ce dansa ya samu gurbin karatu a jami’a da kuma ake gab da fara tantance su sai dai rashin sakamakon jarabawar l na neman yiwa yaron nasa kafar ungulu wajen samun gurbin karatu.
Ya ce tuni aka saki sakamakon jarabawar na makarantu masu zaman kansu, amma har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudaden daliban da suka zana jarabawar a makarantun gwamnati.
Ya kara da cewa idan har gwamnati ta gaza biyan kudin don sakarwa ‘ya’yan su sakamakon jarabawar to la shakka  za su rasa guraben karatu a jami’a a wannan shekarar.
Balarabe Musa mahaifine da yaron sa ya rubuta NECO a Kwalejin Rumfa ya ce rashin baiwa ilimi muhimmanci ne yasa har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudin jarabawar.
Ya kara da cewa ya kamata gwamnati ta duba halin da ‘ya’yansu ke ciki musamman yadda suke neman rasa guraben karatu.
Sadiya Hassan ta ce dama can gwamnatin jihar Kano ta saba yin jinkiri wajen biyan kudin jarabawar dalibai a jihar Kano.
Ta ce bai kamata a ce ana samun tasgaro a irin wannan al’amari ba duba da cewa hakan na kara haddasa lalacewar ilimi.
” Yarinyata ta samu gurbin karatu amma kaga idan ba taje da takardun shaidar kammala sakandireba ba za a tantance ta ba.
” Sai ta kara jiran wata shekarar tukunna a irin wannan ne kuma sai kaga karatun yara ya lalace,” a cewar ta.
Binta Garba da ‘yar ta ke karatu a makarantar sakandire ta Liman Idris Maikalwa a unguwar Na’ibawa ta ce tana rokon gwamnatin jihar Kano da tayiwa Allah da Annabi ta biya kudin jarabawar ‘ya’yan su.
“Saidai fa muka biya gwamnati kudin rubuta jarabawar nan naira dubu 12 da 500 kowa hakama nima na biyawa yarinya ta.
“Mun riga mun biya kudin mu amma meyasa gwamnati zataki biyan hukumar kudin don Allah a taimaka a biya don su samu su shiga Jami’a,” a cewar ta.
Sani Salisu Dan hassan shine shugaban kungiyar iyayen yara ya ce za su je duk inda ya dace don tabbatar da cewa an saki sakamakon jarabawar daliban.
Ya kara da cewa wannan rikon sakainar kashi ne da ake yiwa ilimi, duk da cewa kwamishinan ilimi yayi alkawari  za a saki sakamakon amma har  yanzu shiru.
Sai dai duk kokarin da muka yi don jin tabakin kwamishinan ilimi na jihar Kano Sanusi Sa’idu Kiru abin ya ci tura.
Sa’idu Kiru ya ce da wakilin namu da ya sameshi a ofis domin jin bayani.
Koda yaje sai kwamishinan ya ce yaje ya ga babbar sakatariyar ma’aikatar, inda itama tace masa ai sunyi waya da kwamishina ya koma ofishin sa.
Saidai duk da tsahon lokacin da ya dauka yana jiran sa amma bai samu damar ganin sa ba.
Wannan na nuna cewa gwamnatin Kano na son yin wasa da hankulan jama’a ne kawai amma Basu da abin fada

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending