Connect with us

KANUN LABARAI

Da gan-gan gwamnati ta ki biyan kudin NECO-Iyayen yara

Published

on

Aminu Abdullahi
Iyayen yara da dalibai na cigaba da kokawa bisa yadda gwamnatin jihar Kano ta gaza biyan kudin jarabawar kammala karatun sakandire (NECO) da dalibai suka rubuta a watannin baya.
Kano Focus ta ruwaito cewa tun a watan Janairun shekarar da muke ciki ne a ka saki jarabawar  ta (NECO)  ta makarantu masu zaman kansu, sai dai sakamakon daliban makarantu gwamnati ya gaza fita a jihar nan.
Wani mahaifi mai suna Abubakar Isma’il da yaron sa ya rubuta jarabawar a makarantar sakandire dake Sabuwar Kofar ya ce dansa ya samu gurbin karatu a jami’a da kuma ake gab da fara tantance su sai dai rashin sakamakon jarabawar l na neman yiwa yaron nasa kafar ungulu wajen samun gurbin karatu.
Ya ce tuni aka saki sakamakon jarabawar na makarantu masu zaman kansu, amma har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudaden daliban da suka zana jarabawar a makarantun gwamnati.
Ya kara da cewa idan har gwamnati ta gaza biyan kudin don sakarwa ‘ya’yan su sakamakon jarabawar to la shakka  za su rasa guraben karatu a jami’a a wannan shekarar.
Balarabe Musa mahaifine da yaron sa ya rubuta NECO a Kwalejin Rumfa ya ce rashin baiwa ilimi muhimmanci ne yasa har yanzu gwamnati ta gaza biyan kudin jarabawar.
Ya kara da cewa ya kamata gwamnati ta duba halin da ‘ya’yansu ke ciki musamman yadda suke neman rasa guraben karatu.
Sadiya Hassan ta ce dama can gwamnatin jihar Kano ta saba yin jinkiri wajen biyan kudin jarabawar dalibai a jihar Kano.
Ta ce bai kamata a ce ana samun tasgaro a irin wannan al’amari ba duba da cewa hakan na kara haddasa lalacewar ilimi.
” Yarinyata ta samu gurbin karatu amma kaga idan ba taje da takardun shaidar kammala sakandireba ba za a tantance ta ba.
” Sai ta kara jiran wata shekarar tukunna a irin wannan ne kuma sai kaga karatun yara ya lalace,” a cewar ta.
Binta Garba da ‘yar ta ke karatu a makarantar sakandire ta Liman Idris Maikalwa a unguwar Na’ibawa ta ce tana rokon gwamnatin jihar Kano da tayiwa Allah da Annabi ta biya kudin jarabawar ‘ya’yan su.
“Saidai fa muka biya gwamnati kudin rubuta jarabawar nan naira dubu 12 da 500 kowa hakama nima na biyawa yarinya ta.
“Mun riga mun biya kudin mu amma meyasa gwamnati zataki biyan hukumar kudin don Allah a taimaka a biya don su samu su shiga Jami’a,” a cewar ta.
Sani Salisu Dan hassan shine shugaban kungiyar iyayen yara ya ce za su je duk inda ya dace don tabbatar da cewa an saki sakamakon jarabawar daliban.
Ya kara da cewa wannan rikon sakainar kashi ne da ake yiwa ilimi, duk da cewa kwamishinan ilimi yayi alkawari  za a saki sakamakon amma har  yanzu shiru.
Sai dai duk kokarin da muka yi don jin tabakin kwamishinan ilimi na jihar Kano Sanusi Sa’idu Kiru abin ya ci tura.
Sa’idu Kiru ya ce da wakilin namu da ya sameshi a ofis domin jin bayani.
Koda yaje sai kwamishinan ya ce yaje ya ga babbar sakatariyar ma’aikatar, inda itama tace masa ai sunyi waya da kwamishina ya koma ofishin sa.
Saidai duk da tsahon lokacin da ya dauka yana jiran sa amma bai samu damar ganin sa ba.
Wannan na nuna cewa gwamnatin Kano na son yin wasa da hankulan jama’a ne kawai amma Basu da abin fada

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Ba bu inda nace nafi Yan Najeriya shan wahalar Tsadar rayuwa, amma ina Fatan matsalar ta zamo tarihi -Dangote

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

Shugaban rikunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya nisanta kansa da wani labari da ake yadawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa yafi yan Najeriya shan wahalar tsadar rayuwa.

Dangote ya tabbatarwa da yan kasa cewa, wasu ne suka dauki nauyin yada labarin domin bata masa suna a daidai lokacin da Yan Najeriya ke cikin halin ‘kaka na kayi’ saboda wahalhalun da ake fama da su .

Sanarwar ta nemi Yan kasar nan da suyi watsi da labarin, inda Dangote yayi fatan kawo karshen matsalar da ake ciki a Najeriya.

“Duk abinda ya shafi yan Najeriya ya shafemu”, inji Sanarwar.

Dangote ya Kara dacewa, ”an kawo maganar faduwar darajar Naira da sayan kaya da Dala ne domin cimma wasu bukatu na kashin Kai bukatun  da basu samu damar biya ba a baya.”

Kamfanin na Dangote na sarrafa siminti da takin zamani da kuma tatar man fetur. A  bangaren kayan abinci kuma, Kamfanin na sarrafa sikari,  gishiri da kayan dandanon girki ne kadai.

“Muma muna siyan muhimman kayan abinchi a kasuwa kamar yarda kowa ke siya don amfanin kanmu da kuma bayarwa wajen  ciyar da al’umma.” Dangote.

 

Shugaban kamfanin yayi mamakin yadda ake neman haddasa sabani tsakanin Kamfanonin Dangote da bangaren gwamnatin tarayya, inda yace shi dan kasuwa ne ba dan siyasa ba, don haka babu inda yayi maganar kalubalantar Gwamnatin tarayya.

“Kamfaninmu ya kasance me bin dokokin kasa a koda yaushe tare da  neman sauki ga al’umma da fatan alheri.”

Saboda haka, sanarwar ta nemi Yan Nigeria su guji daudar sakon da yake ba daga kamfani yake kai tsaye ba, tare da yada  rade-radi da jita-jita.

Continue Reading

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Trending