Connect with us

Hausa

Rashin kasuwa ya sa ma su sayar da zo6o komawa sana’ar kunu

Published

on

Aminu Abdullahi

Kasuwar zobo da kunun aya da lemo da kuma lamurje na neman 6acewa a jihar Kano biyo bayan hana sayar da kayan hadin lemukan da gwamnatin jihar tayi.

Kano Focus ta ruwaito yadda wasu ma su sana’ar zo6o suka koka bisa yadda a yanzu sana’ar ke neman rugujewa sakamakon rashin masu siye.

Talatu Hassan ta ce ada tana yin cinikin zobo na naira dubu uku a kowace rana saidai a yanzu dakyar take sayar da na Naira dari biyar sakamakon rashin ma su siye.

Ta kara da cewa kayan hadin suna da matukar tsada kuma ba ko ina ake samun su ba sakamakon haramta sayar da su da akayi.

” Idan munje kasuwar ma a boye ake siyar mana da su wani lokacin ma haka muke dawowa ba tare da mun siyo ba.

” Jarina ya karye kowa yana jin tsoron siya don kada ya kamu da wata annoba a zahirin gaskiya muna cikin wani hali,” a cewar ta.

Aisha Lawan ta ce tana saidai zo6o da lemo da kunun aya na Naira dubu hudu kafin bullar annobar da ake zargin sinadaren hadawa ne suka haddasata.

Saidai ta ce a yanzu tana sayar da iya zo6o ne kawai ba kuma tare da ta sanya masa sinadaren da ta saba sawa a baya ba.

“Yanzu ba a siyar dasu sai ansha wahala ake samu ina yin zo6o na dari uku ko biyar ne a kullum shima da siga kawai nake hadashi.

“Gaskiya a yanzu yafi tsada tunda ba bu kayan hadi dake saka shi zaki, kawai iya dafaffen Zobo ne da sikari,” inji ta.

Ta kuma ce kamata yayi gwamnati ta samar da doka mai tsauri da za a hukunta duk wanda aka kama yana saida sinadaren da suka lalace maimakon haramta siyarwa gaba daya.

” Kaga yanzu azumi na zuwa kuma mun fi yin ciniki da azumi fiye da yadda muke yi a baya, don ni na yanke shawarar fara tuyar awara tunda yanzu ba bu kasuwar zo6o,” a cewar ta.

Rukayya Abdullahi ta ce yanzu ta koma sana’ar sayar da awara da Kunu saboda daina siyan zobo da aka yi.

“Tun daga lokacin da aka ce annobar nan ta bulla kuma a sanadiyyar kayan hadin zobo, nake tafka a sara.

” Dole ce ta sanya na koma sana’ar saida kunun tsamiya da awara domin idan na zauna ba bu mai ba ni,” inji ta.

” ya”ya na uku kuma mahaifinsu ya rasu shekaru biyar da suka gabata,” a cewar Rukayya.

A na su bangaren wasu mutane sun bayyana fargabar da suke da ita na shan Zobo.

Saifullahi Usman ya ce duk da cewa mahukunta na alakanta annobar data faru da shan zobo wanda aka hada da sinadaren da suka lalace amma har yanzu yana siya ya sha.

Ya ce a yadda ake zafi a gari yana bukatar abinda zai sanyaya masa makoshi mai zaki kuma bashi da halin da zai sayi lemo dan kamfani wanda hakan tasa yake cigaba da siyan dan hadi,” a cewar sa.

” Ni ba zan iya kashe fiye da naira dari ba don kawai nasha lemon roba na kamfani na gwammace nasha zobo na Naira hamsin na hada da abincin dari da hamsin.

Kullum sai na siya amma dai yawan sa bai kai na da, da nake siya ba,” inji shi.

Zainab Jibril ta ce daga lokacin da annobar ta bulla zuwa yanzu bata kara shan wani abu da tasan ana hadawa da sinadarin ba.

Ta ce wani lokacin ma takan gwammacewa ta hada da kanta maimakon siyan na waje.

“ina fata a shawo kan wannan matsala kafin azumi, don al’umma za su shiga cikin wani hali matukar aka tafi a haka,” inji ta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Trending