Connect with us

Hausa

Shigar Osinbajo masallaci da takalmi ya tada kura a Kano

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Al’umma a Kano na ci gaba da yin tofin ala tshine ga mataimakin shugaban kasa farfesa Yemi Osinbajo bayan da ya shiga masallaci da takalmi.

KANO FOCUS ta ruwaito mataimakin shugaban kasar ya zo Kano ne ranar Talata domin halartar taron tunawa da Sardaunan Sokoto da kuma ta’aziyyar manya da suka rasu.

An dai hango hoton mataimakin shugaban a masallacin Darul Hadith da ke Unguwar Tudun Yola sanye da takalmisa akan kujera, bayan da ya ke ta’aziyyar Dr Ahmad Ibrahim BUK da ya rasu a Juma’ar Makon jiya.

Kodayake galibin masu yin tofin alatsinen na dora laifin ne akan gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da ministan sadarwa Isa Ali Pantami da suka gaza nusar da mataimakin shugaban kasar bukatar cire takalminsa yayin shiga masallaci.

A cewar Yasir Ramadan Gwale “Obama ma da zai shiga Masallaci sai da ya cire takalmi, watakila saboda ya girmama Musulmin da suke Sallah a ciki saboda ya san suna cirewa in zasu shiga.

“Amma shi Osinbajo ba wanda ya iya ce masa ya tube takalmi, Musulmi basa Sallah da takalmi akan dadduma.

“Gaskiya cin fuska ne ana kallonsa da takalmi amma ba wanda ya nuna masa ya cire alhali duk ‘yan tawagar kowa ya cire nasa da zai shiga.

“Abin tambaya anan Masallacin Villa da Shugaban kasa idan zai shiga sai ya cire takalmi, shin in dalili yasa Osinbajo zai shiga, shima da takalminsa zai shiga alhali shugaban kasa ya cire nasa a waje?

“Ya kamata ace Mataimakin shugaban kasa ya zama very diplomatic a lokacin da yake neman Musulmi su yarda da shi saboda yana da bukata a 2023” a cewar Yasir Ramad Gwale.

Shi kuwa Bashir Muhammad cewa ya yi shiga Masallaci da takalmi mai tsafta ba Laifi Bane.

“Haƙiƙa hotunan da ake ta yadawa, ba ‘wai’ tayar da hankali suke yi na sosai ba – sabida ba akan Osinbajo aka fara ganin haka ba.

“To amma, hakan ba ya nufin cewa duk lokacin da wani ya aikata haka, ba za a kalle shi a matsayin wanda bai aikata wani na ba-wai ba.

“Ko da shiga cikin Masallaci da takalmi (idan musamman ana da yaƙinin cewa yana da tsarki) ba laifi ko matsala bane.

“Yana da kyau ace su Ganduje da Pantami, sun fada masa cewa “ranka ya dade, ana dan cire takalmi idan za a shiga.”

“Wannan kuwa, sabida martaba Masallatan da muke dasu; da kuma kyakkyawar tarbiyyar da muke ita, ta tsaftace wuraren bautar mu” a cewar Muhammad Bashir.

Shi kuwa Ali Imam ya wallafa cewar baya goyon bayan shiga masallaci da takalmi da mataimakin shugaban kasa Osinbajo ya aikata.

Sai dai ya ce wasu na fakewa da hakan suna cin zarafin Gwamnan Abdullahi Umar Ganduje tare da dora masa laifi.

“Dama karamin sani kukumi ne. Wanda idan muka ratsa duniyar ilmi za mu ga cewa shiga masallaci da takalmi ba aibu ba ne.

“Akwai nassosin da suka nuna yin sallah da takalmi ma babbar sunnah ce matukar babu najasa a tattare da shi.

“Bukhari da Muslim sun rawaito cewa Sa’id Bin Zaid ya tambayi Sayyaduna Anas RA ko Manzon Allah SAW ya kasance yana sallah da takalmi? Sai ya amsa cewa Eh yana yi.

عن أبى سلمة سعيد بن زيد قال: سألت أنساً: “أكان النبي -صلى الله عليه وسلم- يصلي في نعليه؟. قال: نعم”.

Abu Dauda ya rawaito cewa daga Shaddadu dan Ausu Manzon Allah ya ce ku sa’ba wa Yahudawa domin su ba sa sallah cikin takalmansu da khuffofinsu.

عن شداد بن أوس رضي الله عنه قال: قال رسول الله -صلى الله عليه وسلم-: “خالفوا اليهود فإنهم لا يصلون في نعالهم ولا خفافهم”

Imam Ahmad da Abu Dauda sun fitar da shi daga Abu Sa’id Alkhudry Manzon Allah SAW ya ce idan d’ayanku ya zo masallaci ya duba takalminsa idan ya ga datti ko kazanta ya tsaftace su, sannan ya yi sallah da takalminsa.

أبو سعيد الخدري أنه قال: قال رسول الله -صلى الله عليه وسلم-: “إذا جاء أحدكم إلى المسجد فلينظر فإن رأى في نعليه قذراً أو أذى فليمسحه وليصل فيهما”.

Abu Dauda ya fitar an karbo daga Abuhuraira RA cewa Manzon Allah SAW ya ce” Idan dayanku ya yi sallah zai iya cire takalminsa, amma kar ya cutar da kowa da hakan, idan ya so zai iya ajiye su tsakanin kafafuwansa ko ya yi sallah suna kafafunsa.”

وما رواه أبو داود من حديث أبي هريرة أن الرسول -صلى الله عليه وسلم- قال: “إذا صلى أحدكم فخلع نعليه فلا يؤذ بهما أحداً، ليجعلها بين رجليه أو ليصل فيهما”

Kazalika hadisi ya inganta Annabi SAW yana jan sahabbansa sallah, sai ya cire takalmin da ke kafarsa. Da sahabbai suka ga haka sai su ma suka cire, bayan an gama sallah sai Annabi SAW ya tambaye su dalilin cire takalmansu sai suka ce sun ga ya cire nasa ne sai su ma suka cire nasu, sai Annabi SAW ya ce Jibrilu ne ya zo ya bayyana min akwai najasa a tare da takalmin sai na cire.

أبو سعيد الخدري أنه قال: “بينما النبي -صلى الله عليه وسلم- يصلي بأصحابه إذ خلع نعليه فوضعها عن يساره، فلما رأى ذلك القوم ألقوا نعالهم، فلما قضى رسول الله -صلى الله عليه وسلم- صلاته قال: ما حملكم على إلقاء نعالكم؟ قالوا: رأيناك ألقيت نعليك فألقينا نعالنا، فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم: إن جبريل عليه السلام أتاني فأخبرني أن فيها قذراً”

Wannan ya sa ake yin sallar Gawa da takalmi. Sai dai hakan ba zai saka na goyi bayan abin da Osibanjon ya aikata ba, amma abun sam bai kai yadda jama’a ke kwaza shi ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending