Connect with us

Hausa

Gajeruwar Tunatarwa Akan Watan Sha’aban

Published

on

Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya bayin Allah! Babban Malamin mu, Ash-Sheikh Sulaiman Ar-Ruhaili yana cewa:

“Yaku masoyana ina yi maku kashedi game da Allah, ku kiyayi Allah, hakika Allah yayi maku ni’imah, kasancewar ya sanya ku cikin wadanda suka riski wannan wata na Sha’aban, alhali kuna cikin koshin lafiya da karfi da alkhairi. Don haka, ku godewa Allah mai girma da daukaka a bisa wannan ni’imar da yayi maku; ku kyautatawa kanku ta hanyar yawaita azumi a wannan wata na Sha’aban, la’alla Allah ya sanya ku cikin wadanda zasu samu Aljannah, a dalilin azumtar wannan wata da kuka yi, kuma ya ‘ƴantar da ku daga azabar wuta. Yaku bayin Allah! Ina yi maku gargadi da kashedi, game da Allah, a bisa wannan ganimar da ya baku. Kada kuyi sakaci da ita, kada kuyi kasala a cikinta. Kuyi rige-rige a cikinta, wurin aikata ayukkan alkhairi. Ku sani, abun sayarwar yana da tsada, hakika abun sayarwar Allah shine Aljannah. Kuma tabbas, kudin sayenta da ake nema a wurin ku, dan kadan ne, ya ku bayin Allah.”

Ya ku masoyana, masu girma! Imam Abubakar Al-Bulkhi Allah yayi masa rahama, ya kasance yana cewa:

“Ku sani, watan Rajab wata ne na shuka, watan Sha’aban kuma wata ne na ban ruwa (wato bayi), watan Ramadan kuma wata ne na girbi.”

Sannan ya kara da cewa:

“Watan Rajab kamar iska ne (wato guguwa), shi kuma watan Sha’aban kamar hadari ne, shi kuma watan Ramadan shine ruwan saman.”

Wani babban Malami daga cikin magabata yana cewa:

“Shekara tana nan kamar bishiya ce, watan Rajab shine lokacin fidda furen ta, watan Sha’aban kuma shine lokacin fidda ‘ya’yanta, watan Ramadan kuma shine lokacin tsinkar ‘ya’yan, kuma muminai sune suka cancanci tsinkan ‘ya’yan. Ga mutumin da ya bakanta littafinsa da zunubai, sai ya faranta shi da tuba zuwa ga Allah a cikin wannan watan, wanda kuma ya bata shekarunsa a banza, to sai ya ribaci abunda ya rage na shekarunsa.”

Uwar Muminai, Ummu na Aisha Allah ya kara yarda da ita, ta ke cewa:

“Manzon Allah ya kasance yana yin azumi a cikin wannan watan, har sai munyi tsammanin ba zai ajiye ba. Sannan idan ya ajiye, har sai munyi tsammanin ba zai dauka ba.”

Sannan ta kara da cewa:

“Ban taba ganin Manzon Allah (SAW) ya azumci wani wata gaba ɗayan sa ba, sai Ramadan. Sannan babu wani wata da Annabi yake yawaita azumi a cikinsa kamar Sha’aban.” [Bukhari da Muslim ne suka ruwaito]

Habib Bin Thabit Allah yayi masa rahamah, ya kasance idan watan Sha’aban ya kama, yana cewa:

“Wannan (watan Sha’aban) shine watan Kurra’u (wato watan makaranta Alkur’ani).”

Amru Bin Kais Al-Mula’i Allah yayi masa rahamah, ya kasance idan watan Sha’aban ya kama, yana kulle shagonsa, ya kebance kansa ga karatun Alkur’ani kawai.

Salmata Bin Kuhail, Allah yayi masa rahamah, yana cewa:

“Ya kasance ana kiran watan Sha’aban da watan Kurra’u.”

Alhassan Bin Shahil, Allah yayi masa rahamah, ya kasance yana yawaita karatun Alkur’ani a cikinsu (wato watan Sha’aban da watan Ramadan) sannan sai yace: “Ya Allah, ka sanya ni a tsakanin watanni guda biyu masu girma.” [Duba littafin, Lata’iful-Ma’arif]

Usamah Bin Zaid yace:

“Ya Manzon Allah, ban ga kana azumtar wani wata kamar yadda kake azumtar Sha’aban ba? Sai Annabi (SAW) yace: Wannan shine watan da mutane suke gafala da shi, tsakanin Rajab da Ramadan, alhali wata ne da ake kai aikin bayi zuwa ga Ubangijin Talikai, shine nike son akai aiki na wurin Allah alhali ina cikin azumi.” [Nasa’i ne ya ruwaito shi, kuma Sheikh Albani ya inganta shi]

An ruwaito daga babban Sahabi, Anas Bin Malik, Allah ya kara yarda da shi yace:

“Sahabban Manzon (SAW), sun kasance idan watan Sha’aban ya kama, sun dukufa kenan akan Alkur’ani, suna karanta shi, sannan su fitar da zakkar dukiyarsu, su karfafi masu rauni, da miskinai, da marasa galihu, a kan azumin watan Ramadan, sannan Musulmai su kira bayinsu, su ce mun yafe maku harajin da ke kanku a cikin watan Ramadan (Abun nufi, wato sun yafe masu. Babu biyan haraji a kansu, har Ramadan ya wuce). Shugabanni kuma su kira ‘yan fursuna, wanda yake da hukuncin haddi sai ayi masa. Wanda kuma laifinsa babu haddi sai a yafe masa, a sake shi ya tafi. Sannan kuma shugabannin al’ummah suna raba kayan arziki ga talakawa” [Duba littafin IKHRAJI-ZAKAT na Ibn Rajab Al-Hanbali]

Ya ku bayin Allah masu girma! Mu dage da addu’a a wannan lokaci mai albarka, musamman a kan matsalolin da suke addabar wannan kasa tamu mai albarka, da kuma yankin mu na arewa. Ku sani, ita addu’a ba ta faduwa kasa banza!

Manzon Allah tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi yace:

“Babu wani Musulmi da za ya roƙi Allah da wata Addu’a wadda babu sabon Allah a cikinta ko kuma yanke zumunta, face sai an bashi ɗayan abubuwa uku: ko dai Allah ya gaggauta bashi abinda ya roƙa nan take, ko kuma Allah ya jinkirta masa sai a lahira a biya shi, ko kuma ya kawar masa da wani mummunan abu da zai same shi. Sai Sahabbai suka ce, lallai zamu yawaita yin addu’a kuwa. Sai Manzon Allah (SAW) yace, Allah zai yawaita.” [Imam Ahmad ne ya ruwaito]

A dage da addu’a ya bayin Allah, sannan a guji yin gaggawa wurin amsawa!

Sannan ‘yan uwana Musulmi, duk yadda za’ayi, kada ku bar zikirorin safiya da kuma na marece, domin zasu kusanta ku ga Allah. Sannan zaku samu kariya daga dukkan abin ƙi, na daga shaidanu da mutane. Kuma kariya ne daga sharrin hassada, da kambun baka, kai da ma dukkan wani abu mai cutarwa!

Ya Allah, ka nuna muna Ramadan muna masu Imani da koshin lafiya.

Ya Allah, kasa muna daga cikin bayin ka da zaka ‘ƴanta a cikin wannan wata mai albarka.

Daga karshe, Abu Darda yana cewa:

“Babban abun tsoro na shine, in tsaya a gaban Allah ranar sakamako, ace da ni, Abu Darda, me kayi da ilimin da ka koya?” [Duba littafin Addaʾu wad-dawa’]

Dan uwa na mai daraja, abun tambaya a nan shine: Shin da ni, da kai, da ke, da ku, da su, mun taba tambayar kawunan mu game da yadda muke sarrafa abunda muka koya na ilimi kuwa? Shin mu ma wane tanadi mu kayi wurin amsa wannan tambayar a gaban Allah, gobe kiyama😭?!

Sannan a kashe, wallahi ina shaida maku cewa, duk wanda yake son ya more wa rayuwar duniya da ta lahira, to yabi Allah…!

Wassalamu Alaikum,

Dan uwanku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, jihar Kogi, Najeriya. Za’a same shi a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending