Hausa
Kano ba ta dace da APC ba – Bello Sharada

Bello Muhammad Sharada
A tarihi Kano gari ne na ilimi. Kano gari ne na addini. Kano gari ne na kasuwanci. Kano gari ne na sarauta. Kano gari ne ‘yanci da walwala da tarbiyya. Kano ana yi mata kirari da Tumbin Giwa, jallabar Hausa ko da me ka zo an fika. Limisliki alfun.

Ka auna tarihin Sarakunan Kano na Hausa da Sarakunan Kano na Fulani. Ka koma yadda Kano take bayan Turawan mulkin mallaka sun zo har suka ci mu da yaki a 1903 da lokacin da aka bamu ‘yancin kai a 1960, da sanda aka kirkiro jihar Kano a 1967, da zamanin soja na Audu Bako da Sani Bello da Ishaya Aboi Shekari kafin a baiwa farar hula mulki a jamhuriya ta biyu a shekarar 1979 da zamanin mulkin Rimi da Abdu Dawakin Tofa da Sabo Bakin Zuwo a tsakanin shekara biyar 1979-1984. Da yanayin da gwamnonin sojoji suka yi mulki a shekara 15 tun daga watan Augusta 1985 har zuwa watan Mayu 1999, aka yi gwamna Hamza Abdullah da Idris Garba da Ahmad Daku da Ndatsu Ummaru da Kabiru Gaya da Abdullahi Wase da Dominic Oneya da Aminu Isa Kwantagora basu saba da tsarin Kano ba sai a shekara bakwai da take hannun Hadimu.
Abin da ya jawo haka, an kauce tsarin Kaka da kakanni na siyasar Kano da tsarinta da dabi’unta. Jihar Kano ta dada sukurkucewa ne a zamanin mulkin APC na Gandujiyya. Duk girman Kano da daukakarta da yawan jama’a da Allah ya hore mata, mutum biyar ne kadai sai abin da suka shata, suka kitsa ko kana so ko baka so. Sun ce lokacinsu ne. Da sannu zasu tafi. Na farko gwamna Ganduje. Na biyu uwargidansa Farfesa Hafsat. Na uku Murtala Sule Garo. Na hudu Abdullahi Abbas. Na biyar Alasan Ado Doguwa. Mataimakin gwamna Ganduje sunansa ma Mota ba Fasinja saboda ba shi da wani tasiri, an ajiye shi safayar taya. Takarar gwamna da aka ba shi dole ce uwar naki. Shi kuma Usman Alhaji Sakataren gwamnati hoto ne. A gefe guda kuma suka dan dosana shugaban majalisar jiha Rt Hon Chidari. Wanda duk bai gamsu ba ya tambayi Dr Baba Impossible.
Babu wani abu da za a yi sai da izinin wadannan mutanen. Rigimar G7 da kafuwar NNPP ita ce kadai ta rage kaifin Goggo da Dan Sarki da Alasan Doguwa. Burin dan Sarki ya zama Sarki, burin Goggo kwamanda ya zama gwamna, burin Ganduje ya zama Sanata ko mataimakin shugaban kasa. Burin Alasan Ado Doguwa ya maye gurbin Femi Gbajabimilla.
SU biyar din nan kowa da bukatar da ta hada su. Zaka gansu jumlatan, amma zuciyoyinsu daban-dabam. Dukkansu suna jifan juna. Murtala ya taba keta Alasan, ya taba cakume Abdullahi Abbas, a kwanan nan kuma Alasan Ado sai da ya mari Murtala a gaban Gawuna kuma a cikin gidansa. Alasan zai iya zagin kowa da sunan siyasa. Hatta Ahmed Aruwa sai da Alasan ya hankade shi a gaban mahaifiyarsa. A gaban Abdullahi Adamu shugaban jam’iyya na kasa na APC da gwamna Ganduje ya hayayyako wa Sardaunan Kano, har suka yi cacar baki da Aliko Dan Shuaiba, aka shiga tsakani. Yan wannan guruf din sune suka tsangwami Barau, an kai matsayin da Sanata Barau bai isa ya zo taro ba a Kano sai dai ya yi harkarsa a Abuja. Kwanan nan Sanata Barau ya baiwa Ganduje kyautar miliyan 150.
Abin da ya nace APC ba ta dace da Kano ba, a wadannan shekarun ne gwamna Ganduje ya kalli manyan masu daraja ya keta musu alfarma, sannan ya kirasu da Dattawan Wukari. A wannan lokacin ne gwamna ya dauki aikin da aka zabe shi domin ya aiwatar amma ya danka shi a hannun uwargidansa, har kuma ta nada wanda zai gaje shi.
An kai matsayin da komai ba a yinsa daidai a Kano a mulkin Ganduje. In kuma ka tanka sai a daureka. Ko a saka wasu karnuka su yi tayi maka haushi. GA Kano garin kasuwanci an yanka kasuwa ko ina ba tsari. Kullum a cikin rigimar fili. Kano garin Sarauta, ita kanta masarautar an yi mata filla-filla, Alasan Ado Doguwa ma Sardaunan kasar Rano ne, da rawaninsa ma ya kwankwashi bakin Murtala. Kano garin malanta, Council of Ulama sai da aka yi mata kishiya, hatta halifancin Tijjaniya sai da aka kutsa ga na Sarki ga na gwamna. Siyasa kuma ba a zancenta, Rarara ya taba zambo da tsulan biri aka yi masa tafi. Ya yi habaici da duna aka yi masa dariya. Ya buga misali da hankaka ana shirin kulle shi.
Babu wani lamarin APC da ake yi cikin adalci. Kowa kuka yake yi. Ga shi kansa Mai gidan APC na kasa babu wani abin alheri mai girma da aka yi wa jama’ar Kano a saboda kauna da biyayya da goyon baya da suke yi masa tsawon shekara 18.
APC bata dace Kano ba. A 2023 Sai an canza da kuri’armu cikin yardar Allah.
Bello Muhammad Sharada jigo ne a Siyasar gidan Malam Ibrahim Shekarau

Hausa
FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.
KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.
Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.
“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”
“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”
SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.
While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.
In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.
There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.
NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.
NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.
