Connect with us

KANUN LABARAI

Mai ya kamata ku sani game da tallafin gwamnati na kiwon jaki-Sheik Daurawa

Published

on

Aminu Abdullahi

Fitaccen malamin addinin musulunci  a Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce haramun ne musulmi ya karbi tallafin kudaden da gwamnati ko bankuna ke bayarwa don kiwon jaki.

Malam Daurawa ya bayyana hakanne yayin zantawarsa da Kano Focus a ranar Litinin.

Wanna dai na zuwa ne bayan da aka yiwa malamin fatawa kan shirin gwamnatin tarayya na baiwa jama’a tallafi domin gudanar da kiwo jakuna.

Ya ce noman jaki ya kasu kasha biyu, akwai noman jaki da akeyi ta hanyar da shari’ar ta amince, shi ne daukar kaya da sauran abubuwa da jaki yakeyi na al’ada.

Sannan kuma akwai noman jaki domin safararsu ga masu ci ko yankawa domin wata bukata.

Ya kara da cewa jaki dadadden abune wanda Allah S.W.A ya ambace shi a cikin alqur’ani, a gurare da dama kuma manzon Allah S.A.W yana da jaki hakama sahabban sa.

Tsohon gwamnan Kano Kwantagora ya rasu

Jahilai ke sukar Fatawar Dr Bashir kan sakin aure a film-Sheikh Umar Sani Fagge

Duk wanda ya saki mace a film ta gida ta saku-Dr Bashir Aliyu Umar

“A kwai lokacin da aka zo yakin Khaibara saboda yunwa da ta damu sahabbai,  har akayi tunanin a yanka jakuna a ci, kuma aka yanka jakunan aka dora sanwa, saida ya tafarfasa ya dauko dahuwa sai annabi S.A.W  ya bada umarnin cewa a zubar da naman a fasa tukunyar.

“Sai wani sahabi yace ko a wanke?  wannan ya nuna cewa anyi yunkurin cin naman jaki annabi ya hana kamar yadda ya tabbata a hadisai ingatattu, a cewar sa.

Malamin ya ce tabangaren abinda ya shafi hukunci an haramta cin jaki a musulunci duk da cewa an samu kauli hudu a cikin mazahabobi akwai mazahabar da ta tafi akan cewa cin jaki haram ne.

Haka zalika yace akwai malaman da sukace cin jaki halal ne, wancan da aka hana an hana ne akan cewa kada a cinye jakuna a wancan lokaci ya zama babu abin hawa.

“Akwai kuma malaman da sukace makaruhine, kamar a mazahabar malikiya, an kawo ruwaya biyu wasu sunce cin jaki makaruhi ne wasu kuma sun ce halal ne,” inji Daurawa.

Sai dai ya ce abinda aka tafi akai shi ne hadisi karara da ya ce annabi S.A.W ya haramta cin naman jakin gida da auren mutu’a .

A don haka idan har gwamnatin tarayya ta baiwa mutum kudi ya kiwata jaki domin suyawaita a cikin al’umma kuma ayi ayyuka dasu irin na al’ada to wannan babu laifi.

Haka zalika ya ce idan mutum ya yi kiwon jakuna domin a rinka siyarwa wadanda za su ci to tamkar yatemakane a ci jakin dashi, kuma addini ya hanashi ya ci ko ya siyar aci.

Ya kara da cewa musamman wadanda suke kaisu kasar China ana kashe su anaci, sannan ayi amfani da fatun su wajen yin wasu sinadarai na magunguna to sun sabawa koyarwar addinin musulunci kuma Allah zai tambayesu akan hakan.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina

Published

on

 

Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.

 

Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.

 

Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.

 

Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).

 

“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.

 

Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.

 

“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.

Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.

 

“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.

 

Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Trending