KANUN LABARAI
An kafa kotunan sauraron korafin zaben kananan hukumomi a Kano

Aminu Abdullahi
Babban jojin jihar Kano Sagir Umar ya kaddamar da kotuna tare da rantsar da alkalan da zasu saurari korafe-korafen zabukan kannan hukumomi da aka gudanar a nan Kano.
Kano Focus ta ruwaito cewa Sagir Umar ya rantsar da alkalan ne a ranar Talata a nan Kano.
Ya ce an kafa kotunan ne bisa dogaro da sashe na 36 sakin layi na 1 na kundin zabukan kananan hukumomin jihar Kano na shekarar 2000 da ya baiwa babban joji ikon kafa kotunan sauraron karar rakin zaben kananan hukumomi.
Cikin wadanda aka rantsar akwai mai shari’a Muhammad M Jibril a matsayin wanda zai jagoranci kotu ta daya, da za ta saurari korafe-korafen zabe.

Sai kuma mambobinsa da suka hadar da Mahmud Shirima da Barista Abubakar Idris Sadiq.
Sai mai shari’a Rakiya Lami Sani da za ta jagoranci kotu ta biyu, inda Kabiru Abubakar da Fatima Isma’il za su kasance a matsayin mambobin kotun.
Haka zalika an rantsar da mai shari’a Ibrahim Musa Karaye a matsayin wanda zai jagoranci kotun daukaka karar zaben, da mai shari’a Jamilu Shehu Sulaiman da kuma Maryam Ahmad Sabo a matsayin mambobin kotun daukaka karar.
Covid-19: Ganduje ya rufe gidajen kallo da na biki
NLC ta ja kunnen Ganduje kan zabtare albashin ma’aikata
Ganduje ya zaluncemu miliyan 80 a albashin Nuwamba da Disamba-ma’aikatan kotu
Mai shari’a Sagir Umar ya hori wadanda aka rantsar da su kasance masu gaskiya da tsoron Allah yayin tafiyar da ayyukan su.
Haka zalika ya ce kotunan na da damar yanke hukuncine cikin kwanaki sittin daga sanda aka gabatar da kara a gabansu, kuma kowane lokaci daga yanzu za su fara aiki.
Ya kara da cewa tun kafin a gudanar da zabe aka kafa ofishin shigar da korafi kamar yadda doka ta tanada.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
