KANUN LABARAI
Tsadar man kuli ta sabba hauhawar farashin kosai da awara a Kano
Aminu Abdullahi
Hauhawar farashin man gyada a Kano ya sabba karuwar farashin kosai da awara da sauran kayan da ake sarrafawa da man gyada.
Kano Focus ta ruwaito a ‘yan kwanakin nan kosai da awara da fanke suka yi tashi gwauron zabo sakamakon karuwar farashin man gyada a fadin jihar.
Binciken da Kano Focus ta gudanar ta gano cewar a baya dai ana sayar da kwalbar man kuli akan N450, da a yanzu kuma ake sayarda kowacce kwalba akan N650 zuwa N700.
Haka zalika a yanzu ana sayar da karamin galan akan N5500, sabanin yadda ake sayar dashi a baya da bai gaza N300 ba.

Kosai N10 duk guda daya
Hajiya Aisha Sulaiman wata mai sana’ar tuyar kosaice a nan Kano, ta ce ya zama dole ta mayar da sakin kosai daga N5 zuwa N10 sakamakon tsadar da man gyada yayi.
A cewarta matukar bata kara farashin ba to ba za ta iya mayar da kudin da ta kashe ba ballantana ta ci riba.
“Ya zama dole nayi hakan, idan ba haka ba bazan maida kudina ba.
“Wake ya yi tsada, muna siyan kwano akan N800 ga kuma mai shima yadda kullum yake kara kudi.
“Mankuli ma ana saida shi ne akan N800, to kaga bamu da zabi tunda ba zamuyi tuya da manja ba.” a cewar ta.
Biyu 50 muke sayar da fanke
Ita ma Rukayya Muhammad da ke zaune a unguwar Tukuntawa dake sana’ar tuyar fanke ta ce kafin karuwar farashin mangyada tana saida fankenta akan naira goma duk guda daya.
Sai dai ta ce a yanzu dole ya sanya take sayarwa aka N50 duk guda biyu.
Ta ce duk da ta kara kudin amma mutane na cigaba da zuwa siya sai dai ba kamar a bayaba, lokacin da take sayarwa akan N10
“Ni kaga jarka nake siya amma wallahi a hakanma dakyar nake maida kudi na, kaima dai kasan yadda abubuwa suke tsada kulllum abubuwan kara kudi suke yi.
“Wasu idan suka zo siya dana fada musu yadda na koma siyarwa sai suyi tafiyar su, basa dawowa, don ranar da na fara canza farashi ma saida nayi kwantai,” a cewar ta.
Munfi sayar da awara akan uku N50
Talatu Gambo dake sana’ar a wara akan titin Gidan Zoo ta ce duk da kudin wake ya karu amma tana siyar da a wararta duk guda daya akan naira goma.
Sai dai ta ce a yanzu da farashin mangyada ya karu ta koma siyarwa akan guda uku naira hamsin.
“Saboda a gefen titi nake ciniki, shiyasa koda na sauya farashi ana cigaba da siya,
“Haka kuma ko yanzu farashin ya ragu to nima zan rage nawa farashin ya koma kamar da.
“Ni dai dana tambaya meyasa kudin mangyadan ya karu sai aka cemin wai yanzu ba a noma gyada, a kasar nan yawanci ana kawo ta ne daga Senegal,” a cewar ta.
In makomar jama’a?
Jama’a da dama da Kano Focus ta zanta dasu kan wannan kari da aka samu, sun nuna rashin jin dadinsu da halin da aka tsinci kai a ciki.
Wani matashi Ibrahim Isma’il da muka iske a layin siyan kosai yace kwanaki uku da suka gabata N5 ya sayi kosan duk guda daya sai dai yanzu ya koma N10.
“Kwana uku da nazo na siyi kosai duk daya N5, amma a yau da na dawo ana saida guda daya N10.
Haka na hakura nasiya saboda iyalina ta damamin koko kuma ba zai shawu ba babu kosai.
“A da ina siyan na N200 amma yau sai da na siyi na N500 saboda farashi ya tashi.” inji Ibrahim Isma’il.
Abubakar Abdulaziz da muka tarar shima yaje siyan kosai cewa ya yi ba zai iya siyan kosai ba a halin yanzu , duba da yadda aka kara masa kudi.
Ya ce ada yana siyan na dari da hamsinne wanda ake bashi duk guda daya a N5 sabanin yanzu da aka ce masa N10.
Ko hakan ya shafi mata a gida?
Sadiya Hassan uwargidace da ke zaune a unguwar Tukuntawa ta ce a yanzu ba a samun man gyada na N50 sabanin yadda a baya ake basu
“A watannin baya N50 ko N100 ta isheni nayi miyar kuka ko miyar shinkafa, amma yanzu sai na saka N150 nake iya siyan man da zanyi girki dashi.
“Kuma kudin cefanen da ake bamu ba karuwa yayi ba, a haka muke riritawa mu girka koda babu dadi don girki ba zai yiwuba idan babu mai, shi kansa yanzu manjan tsada yake yi,” inji Sadiyya.
Jamila Muhammad cewa ta yi a yanzu suna yin girkine kawai da hikimomi tunda dai abubuwa sun ta’azzara.
“Gaskiya ni kaga mai gidana baya son girki da manja, kuma yanzu mangyadan ya yi tsada, hakuri kawai ake y, ni a yanzu ma nafi jika garin kwaki musha da yarana, saboda tsadar da man yayi,” a cewar ta
Ko me dillalan man ke cewa?
Abdullahi Adamu dake sana’ar sayar da mangyada a kasauwar Rimi ya ce watanni biyu da suka gabata suna siyar da mangyada duro guda akan N170,000, amma a yanzu suna sayarwa ne aka N190,000.
Ya kuma ce suna sayarda yaluwar jarka akan N19,500, sai kuma karamin galan suna sayarwa akan N4000 sai kuma kwalba daya akan N650.
Ya kuma ce tashina man na da nasaba da gyadar da ake sarrafawa domin yin mangyadar, ana shigo da ita ne daga kasashen ketare.
A cewarsa hakan ya farune sakamakon karancin noman gyada a jihar nan da ma kasa baki daya.
Saidai ya ce farashin yana hawa da sauka ne a galibin lokuta.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
