Connect with us

KANUN LABARAI

Yajin aikin ‘yan sahu ya jawowa daliban jami’a maimata shekara

Published

on

Aminu Abdullahi

Yajin aikin matuka baburan Adai-daita Sahu ya jawowa dalibai da dama asarar jarrabawa a jami’o’i da manyan makarantun jihar Kano da hakan ke nuna za su maimaita shekara kacokan.

A zantawar Kano Focus da wasu daga cikin daliban da suka tafka asarar, sun bayyana yadda suka shiga wani hali sakamakon yajin aikin da masu dan Sahun suku shiga.

A cewarsu galibinsu basu samu damar rubuta jarrabawa ba, kuma makarantunsu ba lallaine su duba halin da suka shigaba, balle a ce za a sake yi musu wata daban.

Zahra Jibril Ibrahim da ke sashin ilimin addinin musulunci a jami’ar Yusuf Maitama Sule ta ce duk kokarin da ta yi na taga ta samu yin jarrabawar amma bun ya ci tura.

Acearta ta fito ne tun karfe takwas na safe daga unguwar Ja’en amma har tazo Dorayi karshen waya ba ta samu abin hawa ba.

Ta kara da cewa dakyar ta samu wani mai kurkura  ya dauke ta zuwa makarantar da shima sai da ya karbi N300 a gurin ta.

Ta kuma ce duk da ta hau kurkura amma bata samu damar rubuta jarabawarba saboda kafin ma ta isa makarantar an kammala jarrabawar.

“Muna da yawa wadanda bamu samu damar rubuta jarabawarba amma mun shirya zamuyiwa makaranta korafi ko za ta bamu damar rubutawa,” a cewar ta.

Yajin aikin ‘yan sahu: Kurkura ta maye gurbin adai-daita a Kano

‘Yan adai-daita sahu bata Kano suke -Bappa Babba

Za a kwace adai-daita sahun duk wanda ya fita zanga-zanga

Ita  ma wata daliba Zainab Mika’il dake Jami’ar Bayero, ta ce tun daga Hotoro farawa ta tako da kafa har saida ta zo Hotoro kwanar Magi sannan ta samu wani mai babur da ya rage mata hanya zuwa Kabuga.

Ta kara da cewa daga Kabugane ta samu a kori-kura ta karasa da ita zuwa jami’ar Bayero domin ta rubuta jarabawa.

Ta ce duk da haka lokacin da ta isa makarantar ta tarar an gama jarabawar baki daya.

” Iya daliban da suke zaune a makaranta ne kawai suka samu damar rubuta jarabawar, amma mu da muke zuwa daga nesa ba muyi ba.

“Amma naji shuwagabannin aji sunce za su bibiyi al’amarin danganin an bamu damar rubutawa koda bayan mun gama jarabawa gaba daya ne,” a cewar ta.

Ta ce ya kamata gwamnati tayi abinda ya dace domin wannan yajin aiki ba kowa yake shafaba face ‘ya’yan talakawa da basu da masu kai su makaranta a mota.

Sadiya Aliyu daliba a kwalejin ilimi ta tarayya dake jihar Kano ta ce rashin abin hawa yasa ta rasa rubuta jarabawar da take tsaka dayi.

“Na tarar da yawan dalibai sun fito daga dakin jarabawa kuma da alama na rasa ta kenan, naje don a bani na rubuta amma ance ta riga ta wuceni.

“Ina fata iya wannan ranarce kawai ba za su cigaba da yin yajin aikinba, don kuwa indai aka cigaba da yin haka to tabbas zan ta rasa rubuta jarabawa ta,” a cewar ta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending