Connect with us

KANUN LABARAI

Yajin aikin ‘yan sahu ya jawowa daliban jami’a maimata shekara

Published

on

Aminu Abdullahi

Yajin aikin matuka baburan Adai-daita Sahu ya jawowa dalibai da dama asarar jarrabawa a jami’o’i da manyan makarantun jihar Kano da hakan ke nuna za su maimaita shekara kacokan.

A zantawar Kano Focus da wasu daga cikin daliban da suka tafka asarar, sun bayyana yadda suka shiga wani hali sakamakon yajin aikin da masu dan Sahun suku shiga.

A cewarsu galibinsu basu samu damar rubuta jarrabawa ba, kuma makarantunsu ba lallaine su duba halin da suka shigaba, balle a ce za a sake yi musu wata daban.

Zahra Jibril Ibrahim da ke sashin ilimin addinin musulunci a jami’ar Yusuf Maitama Sule ta ce duk kokarin da ta yi na taga ta samu yin jarrabawar amma bun ya ci tura.

Acearta ta fito ne tun karfe takwas na safe daga unguwar Ja’en amma har tazo Dorayi karshen waya ba ta samu abin hawa ba.

Ta kara da cewa dakyar ta samu wani mai kurkura  ya dauke ta zuwa makarantar da shima sai da ya karbi N300 a gurin ta.

Ta kuma ce duk da ta hau kurkura amma bata samu damar rubuta jarabawarba saboda kafin ma ta isa makarantar an kammala jarrabawar.

“Muna da yawa wadanda bamu samu damar rubuta jarabawarba amma mun shirya zamuyiwa makaranta korafi ko za ta bamu damar rubutawa,” a cewar ta.

Yajin aikin ‘yan sahu: Kurkura ta maye gurbin adai-daita a Kano

‘Yan adai-daita sahu bata Kano suke -Bappa Babba

Za a kwace adai-daita sahun duk wanda ya fita zanga-zanga

Ita  ma wata daliba Zainab Mika’il dake Jami’ar Bayero, ta ce tun daga Hotoro farawa ta tako da kafa har saida ta zo Hotoro kwanar Magi sannan ta samu wani mai babur da ya rage mata hanya zuwa Kabuga.

Ta kara da cewa daga Kabugane ta samu a kori-kura ta karasa da ita zuwa jami’ar Bayero domin ta rubuta jarabawa.

Ta ce duk da haka lokacin da ta isa makarantar ta tarar an gama jarabawar baki daya.

” Iya daliban da suke zaune a makaranta ne kawai suka samu damar rubuta jarabawar, amma mu da muke zuwa daga nesa ba muyi ba.

“Amma naji shuwagabannin aji sunce za su bibiyi al’amarin danganin an bamu damar rubutawa koda bayan mun gama jarabawa gaba daya ne,” a cewar ta.

Ta ce ya kamata gwamnati tayi abinda ya dace domin wannan yajin aiki ba kowa yake shafaba face ‘ya’yan talakawa da basu da masu kai su makaranta a mota.

Sadiya Aliyu daliba a kwalejin ilimi ta tarayya dake jihar Kano ta ce rashin abin hawa yasa ta rasa rubuta jarabawar da take tsaka dayi.

“Na tarar da yawan dalibai sun fito daga dakin jarabawa kuma da alama na rasa ta kenan, naje don a bani na rubuta amma ance ta riga ta wuceni.

“Ina fata iya wannan ranarce kawai ba za su cigaba da yin yajin aikinba, don kuwa indai aka cigaba da yin haka to tabbas zan ta rasa rubuta jarabawa ta,” a cewar ta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Trending