Connect with us

KANUN LABARAI

Mauludi: ‘yan daba sun kashe matashi a Kano

Published

on

Aminu Abdullahi

Wasu gungun ‘yan daba a unguwar Sani Mainagge da ke cikin birnin Kano a karamar hukumar Gwale sun kashe wani matashi mai suna Auwalu Halilu a yunkurinsu na yi masa kwace bayan ya taso daga mauludi.

Kano Focus ta ruwaito al’amarin ya faru ne a daren ranar Lahadi ya yin da ake tsaka da yin Mauludi a yankin.

shaidun gani da ido sun ce ‘yandaban na fakewa ne a cikin makabartar Gwale su kuma tare dukkanin wanda ya taso daga wurin mauludi ko kuma zai wuce ya tafi harkarsa su yi masa kwace.

A cewar Muhamad Shehu ‘yan daban sun tare Auwalu Halilu ne cikin dare da nufin yi masa, suka kuma soke shi da hakan ya yi sanadiyyar ransa.

Ya ce tun da aka fara mauludi ‘yan daban ke fakewa cikin taron masu mauludin sun aikata ta’asarsu.

Malam Shehu ya ce ‘yan daban sun mamaye unguwar ne ta Sani Mainagge a daren Lahadin da misalin karfe biyu na dare har zuwa karfe uku suna cin karensu ba babbaka.

Ya ce ya samu tsagewar kashi sakamakon saran da ‘yan daban sukayi masa.

Sa’idu Ahmad dan uwa ne ga marigayin, ya ce ayyukan ‘yan daban ya dade yana addabarsu a unguwar, a cewarsa wani lokacin ma har gidajen jama’a suke shiga.

“Munyi iya yin mu amma abin yaci tura muna kira da a dauki mataki.

Anata bagaren mahaifiyar mamacin, Naja’atu Musa Sheka tayi kira ga mahukunta dasu kwato mata hakkin danta.

a cewarta ko kadan  ‘danta bai aikata laifin komai ba amma an rabashi da duniya.

Ta kara da cewa bayan da aka sari ‘dan nata sun sanar da hukumar ‘yan sanda.

“Muna da yara da yawa ya kamata mahukunta su kawo karshen wannan al’amari.

A cewar ta za su zuba idanu su ga hukuncin da jami’an tsaro za su dauka wajen nemo hakkin danta.

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending