Connect with us

KANUN LABARAI

Ko al’umma a Kano za su rungumi sabon tsarin zabe ta internet

Published

on

Aminu Abdullahi

Al’umma a jihar kano na cigaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da batun fara gudanar da zabe ta kafar sadarwa ta yanar gizo.

Wanan ya  biyo bayan bukatar da majalisar dattijai ta kasa ta bijoro da shi a makon da ya gabata na a sauya fasalin tsarin zaben kasar nan daga yadda ake gudanar da shi zuwa na Internet.

Kano Focus ta jiyo ra’ayoyin wasu mutane a sassa daban daban na jihar nan kan irin kallon da suke yiwa sabon tsarin.

Alfanunsa.

Malam Aminu Bello ma zaunin unguwar Dorayi ne a nan Kano, ya ce maida zaben ta internet nada matukar muhimmanci, a cewarsa hakan zai rage magudin zabe da cinkoson al’umma da kuma rikici a filayen zabe.

Ya ce duk da akwai karancin ilimin internet ga fi yawa ga al’ummar kasar nan musamman ma a kauyuka, amma gwamnati zata iya samar da cibiyoyin da za a rika horas da mutanen kauye kan yadda za su yi zaben tun kafin zaben.

Shi ma wani mai suna Usman Yahuza Usman mazaunin Unguwar Sabon Titi ya ce yin zaben ta yanar gizo zai saukakawa al’umma yin zabe kuma cigaba ne kamar yadda akeyi a sauran kasashen da suka ci gaba.

Ya ce da yawa masu tattara kuri’a kan canza alkaluman zabe kuma wani sa’in ma akan sace akwatunan zabe, amma yin zabe ta yanar gizo zai kawo karshe wannan dabi’a.

Rashin alfanunsa

Saidai wata mai suna Kairat Mustapha dake unguwar Koki a nan Kano ta ce kokadan bata goyan bayan amfani da yanar gizo wajen yin zabe.

Khairat tace irin wannan tsarin sam bai dace da irin al’ummar kasar nan ba.

A cewarta, hakanma ba a kwashewa lafiya ballantana a ce za a mayar da zaben ta kafar internet.

Ta ce yin zabe ta yanar gizo ba zai hana rigingimun da ake yi lokacin zabe ba.

Saboda galibi anfi samun  rigingimu bayan zabe wanda sunfi na runfunan zabe.

Abdul’Aziz Mukhtar dake zaune a unguwar Birget cewa yayi kasar nan bata da network mai karfi da za ta iya aiwatar da zabe ta yanar gizo ba.

“Muna da masu yin kutse a cikin yanar gizo wadanda za su iya batawa.

“Hakan gaskiya ba zai haifar da da mai ido ba.”

Matsalar kasar na kwaikwayo.

Farfesa Kamilu Sani Fagge masanin kikiyya siyasa ne a jami’ar Bayero da ke nan Kano ya ce matsalar kasar nan shi ne kwaikwayo wadanda suka riga suka ci gaba.

Farfesa Kamilu ya ce kiran da majalisar dattawa tayi na sauya tsarin za be batayi la’akari da halin da kasar nan take ciki ba, da kuma halin ‘yan siyasar kasar nan.

Ya kara da cewa kasashen da suka cigaba basu dauki zabe amatsayin ko ta mutu ko tayi rai ba kamar yadda yake a kasar nan.

“Yin wannan tsari zai jefa kasar nan cikin matsala sosai.

“Munga yadda ake murde zaben da mutane kesa hannu su yi. Kaga yadda ake magudi iri-iri, to idan ance za a yi zabe ta gidan waya ko na’ura mai kwakwalwa to zai sa mutane suyi rashin gaskiya,” a cewar sa.

Ya kuma ce mafi akasarin mazabun dake jihar nan a kauyuka suke inda babu wuta kuma suke da karancin ilimin na’ura mai kwakwalwa, inda ya ce yin hakan tamkar take musu ‘yancine.

Malam Fagge ya kara da cewa yin hakan abune da zaici kudi sosai ba kuma tare da samun biyan bukata ba, adan haka barin sa shi ne yafi alkairi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Ba bu inda nace nafi Yan Najeriya shan wahalar Tsadar rayuwa, amma ina Fatan matsalar ta zamo tarihi -Dangote

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

Shugaban rikunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote ya nisanta kansa da wani labari da ake yadawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa yafi yan Najeriya shan wahalar tsadar rayuwa.

Dangote ya tabbatarwa da yan kasa cewa, wasu ne suka dauki nauyin yada labarin domin bata masa suna a daidai lokacin da Yan Najeriya ke cikin halin ‘kaka na kayi’ saboda wahalhalun da ake fama da su .

Sanarwar ta nemi Yan kasar nan da suyi watsi da labarin, inda Dangote yayi fatan kawo karshen matsalar da ake ciki a Najeriya.

“Duk abinda ya shafi yan Najeriya ya shafemu”, inji Sanarwar.

Dangote ya Kara dacewa, ”an kawo maganar faduwar darajar Naira da sayan kaya da Dala ne domin cimma wasu bukatu na kashin Kai bukatun  da basu samu damar biya ba a baya.”

Kamfanin na Dangote na sarrafa siminti da takin zamani da kuma tatar man fetur. A  bangaren kayan abinci kuma, Kamfanin na sarrafa sikari,  gishiri da kayan dandanon girki ne kadai.

“Muma muna siyan muhimman kayan abinchi a kasuwa kamar yarda kowa ke siya don amfanin kanmu da kuma bayarwa wajen  ciyar da al’umma.” Dangote.

 

Shugaban kamfanin yayi mamakin yadda ake neman haddasa sabani tsakanin Kamfanonin Dangote da bangaren gwamnatin tarayya, inda yace shi dan kasuwa ne ba dan siyasa ba, don haka babu inda yayi maganar kalubalantar Gwamnatin tarayya.

“Kamfaninmu ya kasance me bin dokokin kasa a koda yaushe tare da  neman sauki ga al’umma da fatan alheri.”

Saboda haka, sanarwar ta nemi Yan Nigeria su guji daudar sakon da yake ba daga kamfani yake kai tsaye ba, tare da yada  rade-radi da jita-jita.

Continue Reading

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending