KANUN LABARAI
Dalilai uku da suka sanya harshen turanci ke danne na Hausa
Zulaiha Danjuma
Wani masani a sashen Kimiyyar harsuna da nazarin harsunan kasashen waje a jami’ar Bayero Dakta Isa Muhammad Inuwa ya bayyana dalilai uku da ke sawa harshen hausa ke bacewa a tsakanin matasan jihar Kano da ma kasa baki daya.
Daktan ya bayyana rashin kwarewa a harshen uwa, da shigowar zamani, da kuma lalata harshen da gangan da sunan gayu a matsayin makaman da ke batar da harshen.
Malamin ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta musamman da jaridar Kano Focus a ranar Litinin.
Rashin iya harshen uwa

Dakta Inuwa ya ce harshen turanci ya yiwa mutane illa da dama a duniya ta yadda ya danne harshen uwa da mutane suka gada iyaye da kakanni.
Haka zalika galibin matasan Hausawa sun fi son a ce sun iya turaci fiye da harshen su na uwa da hakan ke tasiri matuka wajen tafiyar da harshen.
“Harshen turanci ya samu karbuwa a kasashe daban-daban, wajen aikin gwamnati, da harkokin cinikayya, kuma masu amfani da shi sunfi kowannen harshe a fadin duniya ta bangaren mu’amala da cinikayya.
“Yadda turanci ke yiwa harshen hausa illa haka yake yiwa wasu harsunan daban.
“Ya ce a yanzu yaro na isa shiga makaranta sai a fara turashi makaranta Nursery, saboda su koyi turanci, bayan basu gama yi kwari a nasu na uwa ba.
“Hakan ta sanya harshen turancin ke dannen na hausan a kowanne lokaci suke yin magana, saboda da shi aka fara ginosu.
Zamani
Daktan ya kara da cewa akwai abubuwa na zamani da suka shigo da kowa ma da turanci ya san su, ba kuma a fassarasu zuwa hausa, kuma matasa basa neman sanin hakan.
“Akwai abubuwa da dama da idan kace a fassara da hausa ka hada kanka da aiki, kamar ‘earpiece’ da ‘charger’ ‘recharge card’ da wasu da dama.
“To irin wadannan suna nan da yawa a cikin harshen hausa, da turancine amma an hausantar da su kuma bama a tunin sanin ma’anar su da hausan.
Lalata harshen da gan-gan
Shehin malamin ya kara da cewa matasa basa son koyar yaren da gan-gan da wasu ma a ganin su cinyewa ce a ce suna kwaba hausa saboda tsananin iya turancin su.
“Matasa yanzu da gan-gan suke bata hausar su saboda da zarar ance ka iya hausa to za a yi maka kallon na da.
“Kamar yadda za kaji wasu da sunan gayu na wasu irin kalamai na bata yaran kamar ‘wayana ne, ‘ulcer na ne’ duka wadannan lamirin mata ne da su amma sai a basu na maza da gangan.
“Haka kuma wasu abubuwan masu sauki kamar randa, tirmi sai kaji wani yana Tambaya wai meye su.
Ta ya za a inganta harshen?
Dakta ya ce iyaye na da muhimmiyar rawar da za su taka don ganin harshen hausa ya ci gaba.
“Iyaye tun a gida ya kamata sun dinga koyawa yaransu Hausa, da zarar sun ji suna fifita turanci akan harshen su.
“Kakannin su ma ya kamata su dinga zama da su suna koya musu hausa, hakan zai taimaka wajen koyon harshen.
Haka zalika likitan ya ce jin wakoki na gargajiya zai taimaka gaya wajen koyon harshen hausa, hadi ta karatun littattafai

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
