KANUN LABARAI
Shin ya kamata a fara siyarwa da jama’a wurin da za su binne matattunsu
Aminu Abdullahi
Biyo bayan karancin da ake samu na wuraren binnen mutane a makabartun da ke jihar nan al’umma na kiraye-kiraye mayarda makabartu tsarin kasuwanci.
A zantawar Kano Focus da wasu daga cikin jama’ar Kano, sun ce ana samun karancin mawadatan da ke iya siyan filaye su kuma bayar sadaka domin a dinga binne jama’a.
Hakan ta sanya da wuya a je binnen mutuma a makabarta a tarar wurin da za a binne shi ba wuri ne da aka taba binne wani ba.
Hakan ta sanya masu kiraye-kirayen ke cewa ya kamata a fara yanka fili na siyarwa domin binne mutane.

Haka zalika bincike ya nuna cewa ba safai gwamnatin ke samar da filaye domin yin makabartu ba.
Idan gwamnatin ta samar a wasu lokutan za a iske dillalai sun sayar.
Abiya dubu goma don binne mamaci
Mukhtar Muhammad Adam mazaunin unguwar Dorayi ne, ya ce kamata ya yi mawadata su rinka siyan fili suna daukar ma’aikata da za su kula da shi ta yadda duk wanda ya zo binne mamaci zai biya kudi.
Ya ce idan har a ka samu wadanda za su rinka siyan fili su gina famfon tuka tuka da biyan ma’aikata to hakan zai sa a dena samun matsalar karancin makabartu da ake fuskan ta a jihar.
“A kalla a ce naira dubu goma za a biya ga kowane mutum da za a binne inaga hakan zai rage matsalar rashin aikin yi da ake fama dashi.
“Idan wani ya yi aka ga ana samun kudi to da yawan mutane za su rinka siyan filaye kuma za a samu yawaitar makabartun,” a cewar sa.
Aliyu Muhammad Ali dake unguwar gidan Zoo cewa ya yi matsala ce babba yadda ake samun makabartu na cika, ba kuma tare da samun sababbi ba.
Ya ce abin takaici ne yadda a yanzu ake samun karancin masu bada makabarta sadaka a cikin al’umma.
Ya kara da cewa tun da dai ana cikin matsalar tsadar rayuwa ta yadda wasu ke kyashin bayar da kyauta to maida tsarin kasuwanci shine mafita.
Sayar da fili dan binne mamata matsala ne
Murtala Mustapha mazaunin hotoro ya ce ana yawan mace -mace kuma makabartun da ake da su sunyi kadan duba da yawan al’ummar jihar Kano.
Ya kara da cewa da yawan gina masallatai da mawadata ke yi kamata ya yi su maida hankali wajen Samar da makabartu duba da cewa masalllatan da ake dasu sunyi yawa.
“Ni bana goyan bayan maida makabartu harkar kasuwanci ,don hakan ba tsari bane kuma mu musulmai an sammu da sadaukar wa.
“A kwai matsala babba matukar aka wayi gari a jihar nan akace sai mutum ya biya kudi zai binne dan uwan sa,” a cewar sa.
Muhammad Dauda a unguwar Hotoro cewa ya yi laifin gwamnati ne na rashin tilastawa masu fitar da filaye a sabbin unguwanni samar da makabarta.
“Mutum ne zai yanka filoti fiye da tamanin ko dari amma ba zai yi adalci ya fitar da filin makabarta ba sai yaga dama ma zai fitar da dan karamin guri a matsayin masallaci.
“Kamatà ya yi gwamnati ta rinka bi duk inda ake fitar da sabbin gurare a ce ana fitar da makabartu,” a cewar sa.
Ke meneni ra’ayin malamai?
Wani malamin addinin musulunci mai suna Ibrahim Siraj Adhama ya ce tun asali al’umma ke samarwa kansu makabartu a cikin birane.
Ya kara da cewa matsalar karancin makabartun tafi yawa ne a cikin birni ba kamar kauyuka ba da mafi akasari suke binne ‘yan uwansu da suka rasu a bayan gidajen su ko wani bangare na gidajen nasu kuma mafi yawa gonakin sune.
Ya ce akwai manyan makabartu a jihar Kano da za su wadaci al’ummar da ake dasu matukar za a gyara tsarin yadda ake binne mamata.
“Makabartar Bakiya dake kusa da masallacin Annabi S.A.W a Madani ana binne mutane a ciki tun Ma’aiki S.A.W yana raye gashi har yanzu.
“Saboda tsarin da suke amfani dashi ba irin namu bane ba a baiwa mamaci gurin zama na dindin din.
“Idan ka cire Sahabbai da sauran manyan mutane duk wanda aka binne ya samu shekaru fatar ta zama kasa sauran kasusuwan tattare su akeyi sai ayi rami daga gefe a binne.
“Gurin kuma sai a sake binne wasu mutanen a ciki amma mu makabartun mu basu kai wadan nan shekarun ba amma ana cewa sun cika,” a cewar sa.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
