Connect with us

KANUN LABARAI

Auren Janine da Sulaiman ya bar baya da kura a Kano

Published

on

Zulaiha Dajuma

Tun bayan da aka daura auren Sulaiman Isa da Janine Sanchez a ranar Lahadin da ta gabata, al’umma a Kano ke ta tofa albarkacin bakinsu.

A zantawar jaridar Kano Focus da wasu matasa a nan Kano sun ce burin da mata ke da shi ne ya sanya ake haurowa har gida ana dauke musu mazajensu.

Ya yin da  wasu kuma sukace  kwadayin mazanne da neman biyan wata bukata ya sanya suke makalewa matan turawan, ya yin da wasu kuma saka ce hadi ne kawai daga Allah.

A soke lefe ko mu daina auren na gida

Wani matashi Abubakar Adamu Damisa ya ce yanzu lokaci ya yi da yakamata mata su cire buri da kwadayi su fuskanci abinda ya ke dai-dai.

“Ni a matsayina na saurayi zan iya cewa abune da muke farin ciki da shi, kuma Allah ya kawo irin su, suyi ta dauke samarin tunda su matanmu na nan burikan su sun fiye yawa”

“Turawa ba ruwansu da lefe da sauran abubuan da suka rufewa mata ido.

“Yanzu sai dai kawai a zo a dau ango ba kamar yadda aka saba gani ana daukan amarya ba.

“Idan matanmu basu dawo sunyi karatun ta nustuba, to tabbas za a fara ci gaba da duko turawa ana kyalesu gaba daya.

To sai dai a cewar wani matashi kuma dan gwagarmaya Aliyu Samb,  auren Sulaiman wani al’amari ne da ya zo da sabon salo.

Ya ce  auren ya nuna yadda zumunci ya ke da kuma damar auratayya a tsakanin muslmi da kuma ahlil kitabi.

“Ita baturiya, shi kuma dan Najeriya, akwai banbanci mutuka a tsakanin su ya zamanto kamar kulla zumunci ne.

“Irin wanna ake fata duniya ta samu, domin zai taimaka wajen wanzar da zaman lafiya a tsakanin kabilu mabanbanta da kuma addinai.

Ba zamu watsar da matan gida ba

Aliyu Samba ya kuma yi watsi da kalaman da ke cewa, mazan Kano za su watsar da matan gida domin su koma auren turawa.

Ya ce ai ba namijin da yake tsallake matar da Allah ya rubuta masa.

Idan baturiya aka rubuto masa to zai aura, idan kuma tamu ta gida aka rubuto masa to komai kwadayin sa da waccan din sai dai ya kalla daga nesa.

“Kaddarar mutune ke tabbata, ba auran matan turai ne zai sa matan mu na gida su kasa auruwa ba, haka auren mu na gida ba shi ne zai sa turawa su ki auruwa ba.

“Mazan turai za su iya zuwa nan su auri mata bakake, anyi, kuma anayi, mazan mu za su iya auran matansu matanmu za su iya auran mazajen su ba laifi bane” A cewar sa.

Kwadayi ne ya kaishi auren baturiya

Ita kuwa wata budurwa anan Kano Amina Adam ta ce, ita dai a fahintar ta kwadayi ne da son cimma wata manufa ya sanya Sulaiman Auren Janine.

Ta ce ta zauna a kasar turawa ta kuma ga yadda suke gudanar da rayuwar soyyayar su, a cewar ta ba ko sahakka lamarin su ba soyayya ba ce, illa nufin cimma wani buri.

“ Ban taba ganin wanan a matsayin soyayya ba, duk da dai jama’a na cewa soyayya ce.

“A matsayina na wadda ta taba zama a turai, duk da dai na san shi bai taba zama kasar turai ba, na ga irin wadannan  aururrukan.

Ana amfani da turawane domin a cimma wani burin na rayuwa, ciki kuwa har da neman takardar zama a turai.

Ta kuma ce dukkanin wanda ke ganin auren Sulaiman ya budewa maza Kofar auren turawa to shakka ba bu yana cikin hadari mai yawa, domin ba zai fahinci al’amarin ba har sai ya shiga cikn sa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Trending