Connect with us

KANUN LABARAI

Hisba ta kama matasa uku a Kano da ta ce sun kulla mata sharri

Published

on

Amniu Abdullahi

Hukumar Hisba ta cafke wasu mutane uku da ta ce sun yi mata kazafin kone shaguna a kasuwar Badume, ya yin da ta kai sumamen hadin gwiwa da hukumar NDLEA a makon jiya.

Kano  Focus ta ruwaito wadanda hukumar ta kama sun hada da Gambo Babangida da Isma’il Ahmad da kuma Abubakar Kanabaro.

Wadanda ake zargin dai sunyi rubutu a shafukan su na Facebook inda suka ce hukumar ta kone musu shaguna ya yin da taje kamen masu aikata badala da ta’amali da miyagun kwayoyi.

Saidai sun lashe aman su bayan da hukumar ta kama su tare da karyata rubutun da sukayi.

Gambo Babangida ya ce tabbas ya janye kalaman sa domin kuwa yasan cewa masu aikin Allah ba za su aikata abinda ya fada ba.

“Nayi kuskure a rayuwa ta da ban taba yi ba, nafi shekara hamsin da bakwai tabbas harshe na ne ya jawomin kuma bazan kara ba,” a cewar sa.

Isma’il Ahmad cewa ya yi maganganun da yaji mutane sunayine ya kaishi ga aikata haka kuma ba tare da yayi bincike ba.

Ya kara da cewa ya yi nadama daga baya don kuwa ba a kone masa shagon sa ba.

Shima Abubakar Kanabaro cewa ya yi jita-jita ce tayi tasiri akan sa har takai ga ya dora a shafin facebook.

“Nima nayi na dama don har ga Allah nagano basu da hannu a cikin abinda ya faru,” a cewar sa.

Ya kara da cewa a shirye suke da a dauke su aikin hukumar Hisbah don kawar da badala da kuma jaddada ayyukan alkairi a tsakanin al’umma.

“Zamu taimakawa Hisbah wajen bincike gurbatattun abubuwan dake faruwa a kasuwar,” a cewar sa.

Da yake nasa jawabin babban kwamandan Hisbah Muhammad Harun Sani Ibn Sina ya ce sun bi diddigin wadanda suka yada labarin na karya ta shafin facebook tare da kamasu.

Ya ce bayan da aka kamasu ne kuma sai suka karya ta kansu.

Ibn Sina ya ce tunda har sun tuba kuma sun amsa laifin su to hukumar za ta yi musu afuwa kamar yadda ta saba.

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending